< Isaiah 52 >

1 Wake up, wake up, Zion! Be strong! Put on your best clothes, Jerusalem, the holy city. Heathen foreigners won't ever enter you again.
Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
2 Shake yourself free from the dust and get up. Sit on your throne, Jerusalem. Throw off the chains around your neck, captive daughter of Zion.
Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
3 This is what the Lord says: You were sold for nothing, and you will be bought back without money.
Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
4 This is what the Lord God says: First of all, my people went to live in Egypt, then Assyria conquered them for no reason.
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
5 What do have I to do now? asks the Lord. My people have been taken into captivity for no reason. Those who rule them mock them, and I'm treated with contempt that whole time, says the Lord.
“Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
6 So I'm going to make sure my people know me; at that time they will know that I am the one who means what he says. Yes, it's me!
Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
7 What a wonderful sight in the mountains is the one running to bring good news, announcing peace and good news, announcing salvation, telling Zion, “Your God reigns!”
Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
8 The city watchmen shout loudly and sing for joy together; they all see the Lord returning to Jerusalem.
Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
9 Let Jerusalem's ruins all sing for joy for the Lord has come to care for his people; he has set Jerusalem free.
Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
10 The Lord has demonstrated his holy power to all the nations; the whole world will see our God's salvation.
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
11 Leave, leave, get out of there! Don't bring anything pagan; come out and leave it all behind. Those of you who carry the Lord's sacred articles are to purify yourselves.
Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
12 But don't leave in a hurry, don't be in a rush as if you're running away, for the Lord will go ahead of you, and he will also protect those at the back.
Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
13 Look: my servant will act wisely; he will be praised highly, he will be elevated in position, and seen as someone people look up to.
Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
14 But many were horrified by him, so disfigured in appearance, no longer looking like a man, so unlike anyone human.
Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
15 He will surprise many nations, and kings will keep quiet because of him—for they'll see what they haven't been told, and they'll understand what they hadn't heard.
haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.

< Isaiah 52 >