< Isaiah 42 >

1 Look! Here is my servant, the one I support; my chosen one who pleases me. I have placed my Spirit on him, and he will show the nations what is right.
“Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.
2 He won't shout or cry out; he won't raise his voice in the street.
Ba zai yi ihu ko ya tā da murya, ko ya daga muryarsa a tituna ba.
3 He won't break a damaged reed; he won't snuff out a smoldering wick. He will faithfully make sure everyone is treated fairly.
Iwan da ta tanƙware ba zai karye ba, ba zai kashe lagwani mai hayaƙi ba. Cikin aminci zai kawo adalci;
4 He won't give up or become discouraged until he has made sure that justice is upheld throughout the world. Even lands overseas will look forward to his teachings.
ba zai kāsa ko ya karai ba sai ya kafa adalci a duniya. Cikin dokarsa tsibirai za su sa zuciya.”
5 This is what God the Lord says, the one who created the heavens and stretched them out, who made the earth and everything in it, who gives breath to the people on it, and life to those who live there:
Ga abin da Allah Ubangiji ya ce, shi da ya halicci sammai ya kuma miƙe su, wanda ya shimfiɗa duniya da dukan abin da ya fito cikinta, wanda ya ba wa mutanenta numfashi, da rai ga waɗanda suke tafiya a kanta.
6 “I, the Lord, have called you to demonstrate what's right, and I will hold your hand. I will take care of you, and give you as a sign of my agreement with the people and as a light to the nations.
“Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
7 You will make the blind see, set free those who are locked up, and lead those who sit in darkness out from prison.
don ka buɗe idanun makafi ka’yantar da kamammu daga kurkuku kuma kunce ɗaurarrun kurkuku masu zama cikin duhu.
8 I am the Lord—that is my name! I do not give my honor to anyone else; I do not give my praise to idols.
“Ni ne Ubangiji; sunana ke nan! Ba zan ba da ɗaukakata ga wani ba ko yabona ga gumaka.
9 Notice that what I foretold has come true, as will the new things I'm saying to you now. I tell you what will happen before it does.”
Duba, abubuwan da sun tabbata, sababbin abubuwa kuwa nake furtawa; kafin ma su soma faruwa na sanar da su gare ku.”
10 Sing a new song to the Lord! Sing praise from everywhere on earth, you who sail on the sea and everything in it, you islands and everyone who lives in them.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, ku yi yabonsa daga iyakar duniya, ku da kuka gangara zuwa teku, da kome da yake cikinsa, ku tsibirai, da waɗanda suke zama a cikinsu.
11 Let the people in the desert and its towns shout; let the people of the villages of Kedar cry out loud. Let the people of Sela sing for joy; let them shout from the mountaintops.
Bari hamada da garuruwanta su tā da muryoyinsu; bari wuraren zaman da Kedar ke zama su yi farin ciki. Bari mutanen Sela su rera don farin ciki; bari su yi sowa daga ƙwanƙolin duwatsu.
12 Let them glorify the Lord and praise him in the islands.
Bari su ɗaukaka Ubangiji su kuma yi shelar yabonsa a tsibirai.
13 Like a mighty warrior the Lord will march out, like a seasoned soldier he goes out with courage. He gives his war-cry, shouting as he battles and defeats his enemies.
Ubangiji zai fita ya yi yaƙi kamar mai ƙarfi, kamar jarumi zai yi himma; da ihu zai tā da kirarin yaƙi zai kuma yi nasara a kan abokan gābansa.
14 “I didn't say anything for a long time, I kept quiet and restrained myself. But now like a woman giving birth, I will moan and gasp and pant.
“Na daɗe ina shiru, na yi shiru na kuma ƙame kaina. Amma yanzu, kamar mace mai naƙuda, na yi ƙara, ina nishi ina kuma haki.
15 I will dry up the mountains and the hills, and make all their greenery wither. I will turn rivers into islands and dry up the pools.
Zan lalatar da duwatsu da tuddai in busar da dukan itatuwansu; zan mai da koguna su zama tsibirai in kuma busar da tafkuna.
16 I will lead the blind along a road they don't know; I will guide them along paths they don't know. I will turn darkness into light before them, and smooth out the rough places. This is what I'm going to do for them; I won't let them down.
Zan yi wa makafi jagora a hanyoyin da ba su taɓa sani ba, a hanyoyin da ba a saba ba zan bishe su; zan mai da duhu ya zama haske a gabansu in kuma mai da ƙasa mai kururrumai ta zama sumul. Abubuwan da zan yi ke nan; ba zan yashe su ba.
17 But those who trust in idols and say to images, ‘You are our gods!’ will be rejected in humiliation and shame.
Amma waɗanda suka dogara ga gumaka, waɗanda suke ce wa siffofi, ‘Ku ne allolinmu,’ za a mai da su baya da kunya.
18 Listen, you deaf people! Look and see, you blind people!
“Ka ji, kai kurma; duba, kai makaho, ka kuma gani!
19 Who is blind like my servant? Who is deaf like my messenger that I send? Who is as blind as the people of the agreement? Who is as blind as the servant of the Lord?
Wane ne makaho in ba bawana ba, da kuma kurma in ba ɗan aikan da na aika ba? Wane ne makaho kamar wanda ya miƙa kai gare ni, makaho kamar bawan Ubangiji?
20 You've looked at many things but have not really seen; you've heard but never really listened.”
Kun ga abubuwa masu yawa, amma ba ku kula ba; kunnuwanku suna a buɗe, amma ba kwa jin wani abu.”
21 Because the Lord does what is right he wanted to show how important and wonderful his instructions were.
Yakan gamsar da Ubangiji saboda adalcinsa ya sa dokarsa ta zama mai girma da kuma mai ɗaukaka.
22 But this people ended up robbed and raided, all of them trapped in holes or hidden in prisons. They have been stolen like loot, with no one to save them from being someone's prize, no one to say “Give them back!”
Amma ga mutanen da aka washe aka kuma kwashe ganima, an yi wa dukansu tarko a cikin rammuka ko kuma an ɓoye su cikin kurkuku. Sun zama ganima, babu wani da zai kuɓutar da su; an mai da su ganima, ba wanda zai ce, “Mayar da su.”
23 Who of you is going to listen to this, or pay attention later on?
Wane ne a cikinku zai saurari wannan ko ya kasa kunne sosai a cikin kwanaki masu zuwa?
24 Who let Jacob be taken as loot; who let Israel be taken by robbers? Wasn't it the Lord who we sinned against? The people weren't willing to follow his ways, and they refused to obey his law.
Wa ya ba da Yaƙub don yă zama ganima Isra’ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Ubangiji ba ne, wanda kuka yi wa zunubi? Gama ba su bi hanyoyinsa ba; ba su yi biyayya da dokarsa ba.
25 So he poured out his furious anger on them, and the violence of war. Even though they were surrounded by flames, but they still didn't understand. The fire burned them up, but they still did not take the situation seriously.
Saboda haka ya zuba musu zafin fushinsa, yaƙi mai tsanani. Ya rufe su cikin harsunan wuta, duk da haka ba su gane ba; ya cinye su, amma ba su koyi kome ba.

< Isaiah 42 >