< Habakkuk 3 >

1 This is a prayer sung by the prophet Habakkuk. On Shigonoth.
Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
2 I have heard what is said about you, Lord. I stand in awe of your work. Lord, revive it in our times; make it known in our times. In your anger, please remember your mercy.
Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
3 God came from Teman; the Holy One from Mount Paran. (Selah) His glory covered the heavens; the earth was full of his praise.
Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
4 His brightness is like lightning; rays flash from his hand from where his power is hidden.
Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
5 Plague goes before him, disease follows at his feet.
Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
6 Where he stands, the earth shakes. When he looks the nations tremble. The ancient mountains shatter, the age-old hills collapse, but his ways are eternal.
Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
7 I saw the tents of Cushan suffering, the tent curtains of the land of Midian tremble.
Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
8 Did you burn with rage against the rivers, Lord? Were you angry with the rivers? Were you furious with the sea when you rode your horses and chariots of salvation?
Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
9 You took out your bow; you filled your quiver with arrows. (Selah) You split the earth open with rivers.
Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
10 Mountains saw you and shook. Water poured down and swept by. The deep called out, lifting high its waves.
duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
11 The sun and moon stood still in the sky as your sparkling arrows flew and your spears flashed bright.
Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
12 Indignant, you marched across the earth, trampling the nations in your anger.
Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
13 You came out to save your people, to save your chosen people. You crushed the head of the house of the wicked, stripping him from thick to neck.
Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
14 With his own arrows you pierced the heads of his warriors, those who came like a whirlwind to scatter me, gloating like those who secretly abuse the poor.
Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
15 You trod upon the sea with your horses, churning up the mighty waters.
Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
16 I shook inside when I heard this; my lips quivered at the sound; my bones turned to jelly; I trembled where I stood. I wait quietly for the day of trouble that will come upon those who attacked us.
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
17 Even though there are no blossoms on the fig trees and there are no grapes on the vines; even though the olive crop fails and the fields produce no harvest; even though there are no animals in the pen and no cattle in the stalls;
Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
18 still I will be happy in the Lord, joyful in the God of my salvation.
duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
19 The Lord God is my strength. He makes me able to walk in the highest mountains, as sure-footed as a deer. (To the music director: with my stringed instruments.)
Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi.

< Habakkuk 3 >