< Habakkuk 1 >

1 This is the message that Habakkuk saw in vision.
Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
2 Lord, how long do I have to cry out for help and you don't listen? I cry out, “Violence!” but you don't save us from it.
Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
3 Why do you force me to see this wickedness and suffering? Why do you just observe such destruction and violence? Arguments and fighting happen right in front of me!
Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
4 As a result the law is paralyzed, and justice never wins. The wicked crowd out those who do right so that the course of justice is perverted.
Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
5 Look around at the nations, watch and be surprised and amazed. Something is going to happen in your time that you wouldn't believe even if you were told.
“Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
6 Watch! I am raising up the Babylonians, a cruel and brutal people who will march across the world to seize other lands.
Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
7 They are fearsome and terrifying, and so proud of themselves that they set their own rules.
Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
8 Their horses are faster than leopards and fiercer than hungry wolves. Their cavalry charges, racing in from far away. Like eagles, they swoop down to eat their prey.
Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
9 Here they come, all intent on violence. Their armies advance in frontal assault as rapidly as the desert wind, capturing so many prisoners they are like sand.
duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
10 They mock kings and scoff at rulers. They laugh in scorn at fortresses—they pile up earth ramps and capture them.
Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
11 Then they sweep on by like the wind and are gone. They are guilty because their own strength is their god.
Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
12 Haven't you existed from eternity past? You are Lord my God, my Holy One, you do not die. Lord, you appointed them to execute judgment; God our Rock, you sent them to punish us.
Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
13 Your eyes are too pure to look upon evil; you cannot stand the sight of wrong. So why do you put up with untrustworthy people? Why are you silent when the wicked destroy those who do less evil than they do?
Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
14 You make people become like fish in the sea, or like crawling insects, that have no ruler.
Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
15 They drag everyone up with hooks, they pull them out with nets, catching them in dragnets. Then they happily celebrate.
Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
16 They worship their nets as if they were gods, making sacrifices and burning incense to them, because by their nets they live in luxury, eating rich food.
Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
17 Will they keep on unsheathing their swords forever, killing nations without mercy?
Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?

< Habakkuk 1 >