< Ezekiel 9 >

1 Then I heard him shout out with a loud voice, “Start the attack, you who are in charge of punishing Jerusalem! Pick up your weapons!”
Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
2 I watched as six men approached from the upper gate that faces north. All of them were carrying battle axes. There was another man with them. He was dressed in linen and had a scribe's writing kit at his side. They entered and stood next to the bronze altar.
Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
3 The glory of the God of Israel rose from its usual place on the cherubim and went over to the Temple entrance. The Lord called out to the man dressed in linen with the writing kit,
To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
4 “Go through the whole the city of Jerusalem and place a mark on the foreheads of those who sighing and mourning at all the disgusting sins that are done there.”
ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
5 Then I heard him tell the others, “Follow him all through the city and start killing people. Don't be kind or merciful to anyone!
Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
6 Kill the old men, the young men and girls, the women and children, but do not go anywhere near those who have the mark. Start at my sanctuary.” So they started by killing the elders who were in front of the Temple.
Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
7 Then he told them, “Make the Temple unclean and fill the courtyards with dead bodies. Go ahead and do it!” So they went and started killing all through the city.
Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
8 While they were busy killing people, I was left by myself. I fell facedown to the ground and cried out, “Lord God, when you pour out your anger on Jerusalem, are you going to destroy everyone who's left in Israel?”
Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
9 “The sins of the people of Israel and Judah are really terrible,” he replied. “The whole country is full of murderers, and those living in the city are criminals. They're saying, ‘The Lord has given up on our country. He can't see what we're doing.’
Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
10 But I certainly won't be kind to them or have mercy on them. I will make sure they suffer the consequences of what they've done.”
Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
11 Then the man in linen with the writing kit returned and reported, “I've done what you told me to do.”
Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”

< Ezekiel 9 >