< Ezekiel 29 >

1 On the twelfth day of the tenth month of the tenth year, a message from the Lord came to me, saying,
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, face towards Pharaoh king of Egypt and prophesy against him and the whole of Egypt.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Tell him that this is what the Lord God says: Watch out, because I'm condemning you, Pharaoh king of Egypt, you great monster lying in your rivers, who says, ‘The Nile belongs to me; I made it myself.’
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 I'm going to put hooks in your jaws and make the fish in your river stick to your scales. I will pull you up out of your river, and all the fish will stick to your scales.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 I will throw you and the fish away, leaving you in the desert. Your body will fall on the ground and be left in the open. It won't be collected or taken to be buried. I'll leave you as food for wild animals and birds of prey.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 Then everyone in Egypt will know that I am the Lord. When you had to deal with the people of Israel you were like a flimsy walking stick made from a reed.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 When Israel grabbed hold of you, you split apart, damaging their shoulder. When they leaned on you, you broke, putting their backs out.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 So this is what the Lord God says: I will attack you with a sword and kill both people and animals.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 Egypt will become an empty wasteland. Then they will know that I am the Lord. Because you said, ‘The Nile belongs to me; I made it,’
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 that's why I'm condemning you and your river. I will ruin Egypt, making it into an empty wasteland all the way from Migdol in the north to Syene in the south, and up to the border with Cush.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 No one, human or animal, will travel that way or live there for forty years.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 I will make Egypt more of a wasteland than any other country, and its towns will lie in ruins for forty years among all the other ruined towns. I will scatter the Egyptians among the different nations and countries.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 However, this is what the Lord God says: After forty years I will gather the Egyptians from the different countries where they were scattered.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 I will bring Egypt out of captivity and take them back to the land of Pathros, where they originally came from. Their kingdom will be insignificant.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 Egypt will be the lowest of kingdoms and won't ever be more important than other nations again. I will bring Egypt down so that it won't ever be able to rule over the nations again.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 The people of Israel won't ever trust in Egypt again; instead they will be reminded them of their sin when they turned to the Egyptians for help. Then they will know that I am the Lord God.”
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 On the first day of the first month of the twenty-seventh year, a message from the Lord came to me, saying,
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “Son of man, Nebuchadnezzar king of Babylon made his army work really hard in the siege against Tyre. The soldiers had their hair worn off their heads, and their shoulders rubbed raw. However, he and his army didn't gain any benefit from Tyre for all the work they did in attacking it.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 So this is what the Lord God says: I'm going to give Egypt to Nebuchadnezzar king of Babylon who will seize everything valuable. He will loot the country, robbing it to pay his army.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 I'm rewarding him for all his work by giving him Egypt because the work they did was for me, declares the Lord God.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 At that time I will give power back to the people of Israel and I will help you speak to them. Then they will know that I am the Lord.”
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 29 >