< Ezekiel 23 >

1 A message from the Lord came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, there were once two women. They were daughters of the same mother.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 They became prostitutes in Egypt. In fact, they were prostitutes from the time they were young. They allowed their virgin breasts to be fondled and their nipples squeezed.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 The older girl was called Oholah, and her sister Oholibah. I married them both and they had sons and daughters. Oholah represents Samaria, and Oholibah represents Jerusalem.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 Oholah prostituted herself while she was still married to me. She wanted to have sex with her lovers, the Assyrians.
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 They were soldiers dressed in blue, leaders and commanders, all of them handsome young men in the cavalry.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 She gave away herself sexually to all the important men of Assyria. She made herself unclean by her worship of all the idols of those men she wanted to have sex with.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 She didn't stop her prostitution that she started in Egypt—men sleeping with her when she was young, squeezing her virgin breasts and using her to satisfy their sexual appetite.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 So I handed her over to her lovers, the Assyrians she wanted to have sex with.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 They stripped her naked, took away her sons and daughters, and killed her with the sword. She became infamous among women, and they punished her.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 Oholibah saw what happened to her sister, but she became even worse than her in her wanting sex and practicing prostitution.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 She also wanted to have sex with the Assyrians: their leaders and commanders, their splendidly-dressed soldiers—all of them handsome young men in the cavalry.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 I saw that she had also made herself unclean—both sisters were doing the same thing.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 However, Oholibah's prostitution was even worse. She saw pictures of Babylonian soldiers wearing bright red uniforms painted on the wall.
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 They were wearing belts on their waists and large turbans on their heads. They all looked like Babylonian officers in Chaldea, the country where they were born.
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 When she saw the paintings of them, she wanted to have sex with them and sent messengers to them in Chaldea.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 The Babylonians came to her and her love bed, and made her unclean with their sexual desire. However, after she had been dishonored by them, she rejected them in disgust.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 When Oholibah so blatantly prostituted herself, exposing herself naked, I turned away from her in disgust, just as I had done to her sister.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 But she practiced even more prostitution, remembering how she'd been a prostitute in Egypt when she was young.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 She wanted to have sex with her lovers who had genitals like donkeys and who ejaculated like stallions.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 You went back to the indecent acts when you were young, when the Egyptians squeezed your nipples and fondled your young breasts.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 So Oholibah, this is what the Lord God says: I'm going to encourage your lovers to attack you, those you rejected in disgust. I will bring them to attack you from every direction:
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 the Babylonians and all the Chaldeans, the men of Pekod, Shoa, and Koa, and all the Assyrians along with them—all handsome young men, leaders and commanders, chariot captains and important officers, all riding horses.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 They will attack you from the north, invading with a great army, chariots, and wagons. They will come with their shields and helmets and surround you. I will hand you over to them for punishment, and they will judge and punish you following their own laws.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 I feel so strongly about what you've done that I will oppose you, and they will treat you very badly. They will cut off your noses and ears, and they will kill those of you who are left. They will take away your sons and daughters as prisoners, and those of you who are left will be destroyed by fire.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 They will tear off your clothes and take your beautiful jewelry.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 I'm going to put a stop to your immorality and prostitution, which started in Egypt. You won't think longingly about those times, and you'll forget all about Egypt.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 For this is what the Lord God says: Believe it when I say that I'm going to hand you over to the people you hate, the ones you rejected in disgust.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 They will treat you with hatred. They will take away everything you've worked for, leaving you stark naked with nothing, so that so that the indecent acts of your prostitution will be exposed. Your immorality and prostitution
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 is why all this has happened to you, because you acted as a prostitute with the nations and made yourself unclean by worshiping their idols.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Because you did what your sister did, I will give you her cup to drink.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 This is what the Lord God says: You will drink from your sister's cup—a large, deep cup. You will be laughed at and insulted. You'll have to endure much of this.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 It will make you drunk and full of grief because it's a cup of that brings horror and destruction, the cup your sister Samaria drank from.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 You will drink it all down, smash it to pieces on the ground, and tear at your breasts. This is what I have spoken, declares the Lord God.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 In summary this is what the Lord God says: Because you have forgotten about me and have ignored me, you will have to experience the consequences of your immorality and prostitution.”
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 Then the Lord said to me: “Son of man, are you going to condemn Oholah and Oholibah? Expose the disgusting things they've done!
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 For they have committed adultery, and they are guilty of murder. They have committed adultery with their idols, and have even offered their children, whom they had for me, as sacrifices to their idols.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 They also did this to me: On the very same day they both made my sanctuary unclean and violated my Sabbaths.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 On very day that they killed their children for their idols, they went my sanctuary and made it unclean. Look at what they did right inside my Temple!
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 They even kept on sending messengers for men to come from far away. When the men arrived, you would get yourselves ready for them by bathing, doing your eye makeup, and putting in your jewelry.
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 You sat on an expensive couch, with my incense and my oil on a table placed in front of it.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 The room was full of the noise of people partying. Drunk men were brought in from the desert along with some common people and they put bracelets on your wrists and beautiful crowns on your head.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Then I said about the old worn-out woman, ‘Now they can have her as a prostitute because that's what she is!’
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 So they had sex with her like a prostitute. They had sex with Oholah and Oholibah, those immoral women.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 But men who believe in what's right will judge them and impose the punishment for committing commit adultery and murder, because they are adulterers and murderers.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 This is what the Lord God says: Have a mob attack them! Make them terrified and rob them.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 The mob will stone them and kill them with their swords, slaughtering their sons and daughters and burning down their houses.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 This is how I will put an end to immorality in the country, and all the women will be warned not to do what you have done.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 They will punish you for your immorality, and you will have to experience the consequences of your idol worship. Then you will know that I am the Lord God.”
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 23 >