< Exodus 21 >

1 “These are the regulations you are to present to them:
“Waɗannan su ne dokokin da za ka sa a gabansu.
2 If you buy a Hebrew slave, he is to work for you for six years. But in the seventh year, he is to be freed without having to pay anything.
“In ka sayi mutumin Ibraniyawa a matsayin bawa, zai bauta maka shekara shida. Amma a shekara ta bakwai, za ka’yantar da shi, yă tafi’yantacce, ba tare da ya biya kome ba.
3 If he was single when he came, he is to leave single. If he had a wife when he came, she is to leave with him.
In ya zo shi kaɗai, zai tafi’yantacce shi kaɗai; amma in yana da mata a lokacin da ya zo, za tă tafi tare da shi.
4 If his master provides him a wife and she has children with him, the woman and her children shall belong to her master, and only the man shall be freed.
In maigidansa ya yi masa aure, ta kuwa haifa masa’ya’ya maza ko mata, matan da’ya’yan, za su zama na maigidan, sai mutumin kaɗai zai tafi’yantacce.
5 However, if the slave formally states, ‘I love my master and my wife and children; I do not want to be freed,’
“Amma in bawan ya furta ya ce, ‘Ina ƙaunar maigidana, da matata, da’ya’yana, ba na so kuma in’yantu,’
6 then his master is to take him before the judges. Then he shall have him stand against the door or doorpost and use a metal tool to make a hole in his ear. Then he shall work for his master for life.
dole maigidansa yă kai shi gaban alƙalai. Zai kai shi ƙofa ko madogarar ƙofa, yă huda kunnensa da basilla, sa’an nan zai zama bawansa duk tsawon kwanakinsa a duniya.
7 If a man sells his daughter as a slave, she is not to be freed in the same way as male slaves.
“In mutum ya sayar da’yarsa a matsayin baiwa, ba za a’yantar da ita kamar bawa ba.
8 If the man who chose her for himself is not pleased with her, he must let her be bought back. He is not permitted to sell her to foreigners, since he has been unfair to her.
In ba tă gamshi maigida wanda ya zaɓe ta domin kansa ba, dole yă bari a fanshe ta. Ba shi da dama yă sayar da ita ga baƙi, tun da yake bai kyauta mata ba.
9 If he chooses to give her to his son, he must treat her as a daughter.
In ya zaɓe ta domin ɗansa, dole yă ba ta duk damar da’ya ta mace take da shi.
10 If he takes another woman, he must not reduce the food and clothing allowances and marital rights of the first.
In ya auri wata mace, ba zai hana wa baiwar abinci da sutura ba, ba kuma zai ƙi kwana da ita ba.
11 If he doesn't give her these three things, she is free to leave without paying anything.
In bai tanada mata waɗannan abubuwa uku ba, sai tă tafi’yantacciya, babu biyan kome.
12 Anyone who hits and kills someone else must be executed.
“Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle a kashe shi.
13 However, if it wasn't intentional and God let it happen, then I will arrange a place for you where they can run to and be safe.
Amma in ba da nufin yă kashe shi ba, sai dai in Allah ne ya nufa haka, to, sai mutumin yă tsere zuwa inda zan nuna muku.
14 But if someone deliberately plans and purposely kills another, you must take them away from my altar and execute them.
Amma in mutumin ya yi dabara har ya kashe wani mutum da gangan, sai a ɗauke shi daga bagadena a kashe shi.
15 Anyone who hits their father or mother must be executed.
“Duk wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
16 Anyone who kidnaps someone else must be executed, whether the victim is sold or is still in their possessions.
“Duk wanda ya saci mutum ya sayar da shi, ko kuwa aka iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi.
17 Anyone who despises their father or mother must be executed.
“Duk wanda ya la’anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
18 If men are fighting and one hits the other with a stone or with his fist, and the injured man doesn't die but has to stay in bed,
“Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya,
19 and then gets up and walks around outside with his walking stick, then the one who hit him won't be punished, Even so, he must still compensate the man for the time lost from his work and make sure that he's completely healed.
idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda ne, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓata masa, yă kuma lura da shi, har yă warke sarai.
20 Anyone who hits their male or female slave with a rod, and the slave dies as a result, must be punished.
“In mutum ya dūke bawansa ko baiwarsa da sanda, sai bawan ko baiwar ta mutu saboda dūkan, dole a hukunta shi,
21 However, if after a day or two the slave gets better, the owner won't be punished because the slave is their property.
amma ba za a hukunta shi ba, in bawan ko baiwar ta tashi, bayan kwana ɗaya ko biyu, tun da bawan ko baiwar mallakarsa ne.
22 If men who are fighting happen to hit a pregnant woman so she gives birth prematurely, but no serious injury occurs, he must be fined whatever amount the woman's husband demands and as permitted by the judges.
“Idan mutum biyu suna faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka za a biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara.
23 But if a serious injury does occur, then you must pay a life for a life,
Amma in akwai rauni mai tsanani, sai a ɗauki rai a maimakon rai,
24 an eye for an eye, a tooth for a tooth, a hand for a hand, a foot for a foot,
ido don ido, haƙori don haƙori, hannu don hannu, ƙafa don ƙafa,
25 a burn for a burn, a wound for a wound, and a bruise for a bruise.
ƙuna don ƙuna, rauni don rauni, ƙujewa don ƙujewa.
26 Anyone who hits their male or female slave in the eye and blinds them must free the slave as compensation for the eye.
“In mutum ya bugi bawa ko baiwa a ido, har idon ya lalace, dole yă’yantar da shi ko ita, maimakon ido.
27 Anyone who knocks out the tooth of their male or female slave must free the slave as compensation for the tooth.
In kuma ya fangare haƙorin bawa ko baiwa, dole yă’yantar da bawan ko baiwar, a maimakon haƙorin.
28 If an ox uses its horns to kill a man or woman, the ox must be stoned to death, and its meat must not be eaten. But the owner of the ox won't be punished.
“In bijimi ya kashe namiji ko ta mace, dole a jajjefe bijimin har yă mutu, ba za a kuma ci namansa ba. Amma mai bijimin ba shi da laifi.
29 But if the ox has repeatedly hurt people with its horns, and its owner has been warned but still doesn't keep it under control, and it kills a man or woman, then the ox must be stoned to death and its owner must also be executed.
In, har an san bijimin da wannan hali, an kuma yi wa mai shi gargaɗi, amma bai ɗaura shi ba, har ya kashe namiji ko ta mace, za a jajjefe bijimin tare da mai shi, har su mutu.
30 But if instead the payment of compensation is required, the owner may buy back his or her life by paying the full amount of compensation demanded.
Amma fa, in an bukace shi yă biya, zai biya don yă fanshi ransa ta wurin biyan abin da aka aza masa.
31 If the ox uses its horns and kills a son or a daughter the same rule is applicable.
Wannan doka ta shafi batun bijimin da ya kashe ɗa ko’ya.
32 If the ox uses its horns and kills a male or female slave, the owner of the ox must pay thirty shekels of silver to the slave's master, and the ox must be stoned to death.
In bijimin ya kashe bawa ko baiwa, mai shi zai biya shekel talatin na azurfa wa maigidan bawan, a kuma a jajjefe bijimin.
33 If someone removes the cover of a cistern or digs one and doesn't cover it, and an ox or a donkey falls into it,
“In mutum ya bar rami a buɗe, ko ya haƙa rami bai kuma rufe ba, sai saniya ko jaki ya fāɗi a ciki,
34 the owner of the pit must pay compensation to the animal's owner and keep the dead animal.
Mai ramin zai biya rashin da aka yi wa mai shi, matacciyar saniyan ko jakin, zai zama na mai ramin.
35 If someone's ox injures another's ox and it dies, they must sell the live one and share money received; they must also share the dead animal.
“In bijimin mutum ya raunana bijimin wani, har ya mutu, sai mutanen biyu su sayar da mai ran, su raba kuɗin daidai, haka ma su yi da mai ran.
36 But if it was known that the ox had repeatedly hurt people with its horns, and its owner had been warned but still didn't keep it under control, full compensation must be paid, ox for ox, but the owner can keep the dead animal.”
Amma fa, in tun can, an san bijimin yana da wannan halin faɗa, duk da haka mai shi bai ɗaura shi ba, dole mai shi yă biya, dabba domin dabba, matacciyar dabbar kuwa tă zama nasa.

< Exodus 21 >