< Deuteronomy 9 >

1 Listen, people of Israel! Shortly you're going to cross the Jordan to enter and take over the country from nations that are larger and stronger than you, that have large towns with walls that reach up into the sky.
Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
2 The people are strong and tall; they are the descendants of the Anakim. You all know about them and you have heard the saying, “Who could ever defeat the sons of Anak?”
Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
3 But you should realize that today the Lord your God is going across ahead of you. He is like a consuming fire; he will destroy them and defeat them ahead of you. You will drive them out and quickly wipe them out, just as the Lord promised you.
Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
4 When the Lord your God has driven them out ahead of you, don't think to yourselves, “It's because I'm such a good person that the Lord has brought me here to take over this land.” No, the Lord is driving out these nations ahead of you because of they're so wicked.
Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
5 It's not because you're so good or moral that you are going to take over their land. No, it's because of their wickedness that the Lord your God is driving out these nations ahead of you, to keep the promise he made to your fathers—m to Abraham, Isaac, and Jacob.
Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
6 You'd better believe that it's not because you're such good people that the Lord your God is giving you this good land to own, because you are stubborn, hard-hearted people.
Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
7 Remember how you provoked the Lord your God in the desert! Don't ever forget it! From the time you left the land of Egypt until you arrived here, you've been constantly rebelling against the Lord.
Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
8 At Horeb you provoked the Lord, making him so angry he was about to destroy you.
A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
9 This was when I climbed up the mountain to receive the tablets of stone, the tablets that recorded agreement the Lord made with you. I stayed on the mountain forty days and forty nights, and I didn't eat or drink anything.
Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
10 The Lord gave me the two stone tablets on which he'd written with his finger everything he'd told you when he spoke from the fire on the mountain when we were all assembled there.
Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
11 After forty days and forty nights, the Lord gave me the two stone tablets, the tablets of the agreement.
A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
12 The Lord told me, “Hurry! Go down immediately, because your people that you led out of Egypt, are committing a terrible sin. They have disobeyed what I told them so quickly! They have made themselves an idol using molten metal.”
Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
13 The Lord also told me, “I have been watching these people, and they really are a stubborn and hard-hearted.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
14 Leave me, so that I can destroy them and wipe out their name completely. Then I will turn you into a nation even more powerful and more important than them.”
Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
15 I went back down the mountain while it was still on fire, carrying the two tablets of the agreement.
Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
16 Then I saw how much you had sinned against the Lord your God by making for yourselves a molten calf. You had disobeyed what the Lord had told you so quickly.
Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
17 I threw the two tablets down, smashing them to pieces as you watched.
Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
18 Then I lay down on the ground before the Lord for forty days and forty nights, just as I had before. I didn't eat or drink anything because of all the sins you had committed by doing what was evil in the Lord's sight, making him angry.
Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
19 I was terrified at how angry and furious the Lord was with you. He was ready to destroy you. But once again the Lord listened to me.
Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
20 The Lord was so angry with Aaron he was ready to destroy him, but right then I prayed for Aaron too.
Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
21 I took that abominable thing, the calf you'd made, and burned it. Then I crushed it up and ground it into dust, and I threw it into the stream that descended from the mountain.
Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
22 But you went on provoking the Lord at Taberah, at Massah, and at Kibroth-hattaavah.
Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
23 When the Lord had you leave Kadesh-barnea, he told you, “Go and take over the country that I've given you.” But you defied the command of the Lord your God. You didn't believe him and you didn't obey him.
Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
24 You have been rebelling against the Lord from the day I first knew you.
Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
25 So I lay down on the ground before the Lord for forty days and forty nights, because the Lord had threatened to destroy you.
Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
26 I prayed to the Lord, saying, “Please Lord, God, don't destroy your people that belong to you, the ones whom you rescued by your great ability and led out of Egypt by your power.
Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
27 Please remember your servants Abraham, Isaac, and Jacob. Please disregard the stubbornness of this people and their wicked sin.
Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
28 If you don't, those people back in Egypt will say, ‘The Lord brought them out to kill them in the desert because he couldn't take them to the land he'd promised them, and because he hated them.’
In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
29 But they are your people, Lord! They belong to you! You led them out of Egypt by your amazing power and might!”
Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”

< Deuteronomy 9 >