< 2 Chronicles 29 >

1 Hezekiah was twenty-five when he became king, and he reigned in Jerusalem for twenty-nine years. His mother's name was Abijah, the daughter of Zechariah.
Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
2 He did what was right in the Lord's sight, just as his forefather David had done.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
3 In the first month of the first year of his reign, Hezekiah opened the doors of the Lord's Temple and repaired them.
A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
4 He summoned the priests and the Levites, and had them gather on the square to the east.
Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
5 He told them, “Listen to me, Levites. Purify yourselves now and purify the Temple of the Lord, the God of your forefathers. Take away from the Holy Place everything that is filthy.
ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
6 For our fathers were sinful, and did what was evil in the Lord's sight. They abandoned him and paid no attention to the Lord's Temple, turning their backs on him.
Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
7 They shut the doors at the entrance to the Temple and put out the lamps. They didn't burn incense or present burnt offerings at the sanctuary of the God of Israel.
Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
8 So the Lord's anger fell on Judah and Jerusalem, and he made them into something appalling, terrifying, and ridiculous, as you can see for yourselves.
Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
9 As a result, our fathers have died in battle, and our sons and our daughters and our wives have been captured.
Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
10 But now I'm going to make an agreement with the Lord, the God of Israel, so that his fierce anger will no longer fall on us.
Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
11 My sons, don't neglect your responsibilities, for the Lord has chosen you to stand in his presence to serve him, and to be his ministers presenting burnt offerings.”
’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
12 Then the Levites went to work. They were Mahath, son of Amasai, and Joel, son of Azariah, from the Kohathites; Kish, son of Abdi, and Azariah, son of Jehallelel, from the Merarites; Joah, son of Zimmah, and Eden, son of Joah, from the Gershonites;
Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
13 from the sons of Elizaphan, Shimri and Jeiel; and from the sons of Asaph, Zechariah and Mattaniah;
Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
14 from the sons of Heman, Jehiel and Shimei; and from the sons of Jeduthun, Shemaiah and Uzziel.
Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
15 They called together the other Levites and all of them purified themselves. Then they went in to clean the Lord's Temple, as the king had commanded, following the instructions as required by the Lord.
Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
16 The priests went into the inner sanctuary of the Lord's Temple to clean it. They removed all the unclean things that they found in the Lord's Temple and placed them in the Temple courtyard. Then the Levites took them out and carried them to the Kidron Valley.
Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
17 They started the work of purification on the first day of the first month, and by the eighth day of the month they had reached the Temple porch. For eight more days they worked on purifying the Temple itself, and finished on the sixteenth day of the first month.
Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
18 Then they went in to tell King Hezekiah, “We have cleaned the entire Temple of the Lord, the altar of burnt offering with all its utensils, and the table of the showbread with all its utensils.
Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
19 We have recovered and purified all the items that King Ahaz threw away during his reign when he was unfaithful. They are now before the Lord's altar.”
Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
20 King Hezekiah got up early, summoned the city officials, and went to the Lord's Temple.
Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
21 They brought seven bulls, seven rams, seven male lambs, and seven male goats as a sin offering for the kingdom, for the sanctuary, and for Judah. The king ordered the priests, the descendants of Aaron, to offer them on the altar of the Lord.
Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
22 So they killed the bulls, and the priests took the blood and sprinkled it on the altar. They killed the rams and sprinkled the blood on the altar. They killed the lambs and sprinkled the blood on the altar.
Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
23 Then they brought the goats for the sin offering before the king and the assembly, who placed their hands on them.
Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
24 Then the priests killed the goats and placed their blood on the altar for a sin offering, to make atonement for the whole of Israel, because the king had ordered that the burnt offering and sin offering were for the whole of Israel.
Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
25 Hezekiah had the Levites stand in the Lord's Temple with cymbals, harps, and lyres, following the instructions of David, Gad the king's seer, and Nathan the prophet. The instructions had come from the Lord through His prophets.
Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
26 The Levites stood with the musical instruments provided by David, with the priests holding their trumpets.
Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
27 Then Hezekiah gave the order for the burnt offering to be offered on the altar. As the burnt offering began, the song of the Lord began at the same time, the trumpets sounded, and music was played on the instruments of David, once king of Israel.
Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
28 All the people in the assembly were worshiping, the singers were singing, and the trumpeters were playing. This continued until the burnt offering was finished.
Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
29 Once the offerings were completed, the king and everyone there with him bowed down and worshiped.
Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
30 Then King Hezekiah and his officials ordered the Levites to sing praises to the Lord using the words of David and of Asaph the seer. So they sang praises with joy, and bowed their heads and worshiped.
Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
31 Then Hezekiah told them, “Now that you have dedicated yourselves to the Lord, come and bring your sacrifices and thank offerings to the Lord's Temple.” So the people in the assembly brought their sacrifices and thank offerings, and everyone who wanted to brought burnt offerings.
Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
32 The total number of burnt offerings they brought was seventy bulls, a hundred rams, and two hundred lambs; all these were to be a burnt offering to the Lord.
Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
33 In addition there were dedicated offerings of six hundred bulls and three thousand sheep.
Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
34 Since there weren't enough priests to skin all the burnt offerings, their Levite relatives helped them until the work was finished and the priests had been purified. (The Levites had been more conscientious in purifying themselves than the priests had.)
Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
35 Apart from the large number of burnt offerings, there was the fat of the friendship offerings, as well as the drink offerings that went with the burnt offerings. In this way the service of the Lord's Temple was restored.
Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
36 Hezekiah and everyone there were so happy at what God done for the people, because everything had been achieved so quickly.
Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.

< 2 Chronicles 29 >