< 1 Chronicles 12 >

1 The following is a list of the men who joined David when he was at Ziklag, still hiding from Saul, son of Kish. They were some of the leading warriors who fought on David's side.
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 They were all skilled archers, and could shoot arrows or slingshots with their right or their left hands. They were relatives of Saul from the tribe of Benjamin.
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 Ahiezer was their leader, then Joash; the sons of Shemaah the Gibeathite; Jeziel and Pelet the sons of Azmaveth; Beracah; Jehu the Anathothite;
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 Ishmaiah the Gibeonite, (a strong warrior among the Thirty, and leader over the Thirty); Jeremiah; Jahaziel; Johanan; Jozabad the Gederathite;
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Eluzai; Jerimoth; Bealiah; Shemariah; Shephatiah the Haruphite;
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Elkanah, Isshiah, Azarel, Joezer, and Jashobeam (they were Korahites);
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 and Joelah and Zebadiah, the sons of Jeroham from Gedor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 Some warriors from the tribe of Gad went over to David's side when he was at the stronghold in the desert. They were strong and experienced warriors, battle-hardened, experts in the use of shields and spears. Their faces looked as fierce as lions, and they ran as fast as gazelles in the mountains.
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Ezer the was the leader, Obadiah (second), Eliab (third),
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Mishmannah (fourth), Jeremiah (fifth),
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Attai (sixth), Eliel (seventh),
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Johanan (eighth), Elzabad (ninth),
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jeremiah (tenth), Machbannai (eleventh).
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 These warriors from Gad were army officers. The least able of them was in charge of 100 men; the best was in charge of 1,000.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 These were ones who crossed the Jordan River in the first month of the year when it overflows its banks. They chased out all the people living in the valley, both to the east and to the west.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 Some others from the tribes of Benjamin and Judah also came to join David at the stronghold.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 David went out to meet them and told them, “If you've come in peace to help me, we can be friends. But if you've come to betray me to my enemies, even though I've done no wrong, then may the God of our fathers see what you're doing and condemn you.”
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 Then the Spirit came upon Amasai, the leader of the Thirty. “We are yours, David, and we are with you, son of Jesse! May peace, prosperity, and success be yours and those who help you, for God is the one who is helping you.” So David allowed them to join him, and put them in charge of his bands of raiders.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 Others came over to David's side from the tribe of Manasseh and joined him when he went with Philistines to attack Saul. However, the Philistine rulers eventually decided to send them away, saying to themselves, “It will cost us our heads if he deserts us and goes over to his master Saul.”
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 The following is a list of the men from Manasseh who went over to David's side as he returned to Ziklag: Adnah, Jozabad, Jediael, Michael, Jozabad, Elihu, and Zillethai, leaders of thousands in Manasseh.
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 They helped David against raiders for they were all strong and experienced warriors and commanders in the army.
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 Men arrived daily to help David until he had a large army, like the army of God.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 This is a list of the numbers of armed warriors who came and joined David in Hebron to turn over Saul's kingdom to him, as the Lord had said.
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 From the tribe of Judah, 6,800 warriors carrying shields and spears.
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 From the tribe of Simeon, 7,100 strong warriors.
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 From the tribe of Levi, 4,600,
mutanen Lawi, su 4,600,
27 including Jehoiada, leader of the family of Aaron, and with him 3,700,
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 and Zadok, a strong young warrior, with 22 members of his family, all officers.
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 From the tribe of Benjamin, from among Saul's relatives, 3,000, most of whom had remained loyal to Saul up until this time.
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 From the tribe of Ephraim, 20,800 strong warriors, each highly regarded in his own clan.
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 From the half-tribe of Manasseh, 18,000 men were designated by name to come and make David king.
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 From the tribe of Issachar came leaders who knew and could understand the signs of the times and what Israel should do—a total of 200 leaders of the tribe together with their relatives.
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 From the tribe of Zebulun, 50,000 warriors. They were fully armed and battle-ready, and totally dedicated.
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 From the tribe of Naphtali, 1,000 officers and 37,000 warriors carrying shields and spears.
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 From the tribe of Dan, 28,600 warriors, all battle-ready.
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 From the tribe of Asher, 40,000 experienced warriors, all battle-ready.
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 From the east side of the Jordan River, from the tribes of Reuben, Gad, and the half-tribe of Manasseh, 120,000 warriors carrying all kinds of weapons.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 All these men came to Hebron dressed for battle, completely committed to making David king. All of Israel agreed that David should become king.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 They stayed three days there, eating and drinking together, for their relatives had provided them with supplies.
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 Their neighbors, even as far away as Issachar, Zebulun, and Naphtali, arrived bringing food on donkeys, camels, mules, and oxen. They had plenty of flour, fig cakes, bunches of raisins, wine, olive oil, cattle, and sheep, for Israel was so happy.
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.

< 1 Chronicles 12 >