< John 1 >

1 From the first he was the Word, and the Word was in relation with God and was God.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 This Word was from the first in relation with God.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 All things came into existence through him, and without him nothing was.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 What came into existence in him was life, and the life was the light of men.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 And the light goes on shining in the dark; it is not overcome by the dark.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 There was a man sent from God, whose name was John.
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 He came for witness, to give witness about the light, so that all men might have faith through him.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 He himself was not the light: he was sent to give witness about the light.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 The true light, which gives light to every man, was then coming into the world.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 He was in the world, the world which came into being through him, but the world had no knowledge of him.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 He came to the things which were his and his people did not take him to their hearts.
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 To all those who did so take him, however, he gave the right of becoming children of God — that is, to those who had faith in his name:
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 Whose birth was from God and not from blood, or from an impulse of the flesh and man's desire.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 And so the Word became flesh and took a place among us for a time; and we saw his glory — such glory as is given to an only son by his father — saw it to be true and full of grace.
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 John gave witness about him, crying, This is he of whom I said, He who is coming after me is put over me because he was in existence before me.
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 From his full measure we have all been given grace on grace.
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 For the law was given through Moses; grace and the true way of life are ours through Jesus Christ.
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 No man has seen God at any time; the only Son, who is on the breast of the Father, he has made clear what God is.
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 And this is the witness of John when the Jews sent priests and Levites from Jerusalem to him with the question, Who are you?
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
20 He said quite openly and straightforwardly, I am not the Christ.
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 And they said to him, What then? Are you Elijah? And he said, I am not. Are you the prophet? And his answer was, I am not.
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 So they said to him, Who are you then? We have to give some answer to those who sent us. What have you to say about yourself?
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 He said, I am the voice of one crying in the waste land, Make straight the way of the Lord, as said Isaiah the prophet.
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 Those who had been sent came from the Pharisees.
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
25 And they put this question to him, saying, Why then are you giving baptism if you are not the Christ, or Elijah, or the prophet?
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 John's answer was: I give baptism with water; but there is one among you of whom you have no knowledge;
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 It is he who is coming after me; I am not good enough to undo his shoes.
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 These things took place at Bethany on the other side of the Jordan, where John was giving baptism.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 The day after, John sees Jesus coming to him and says, See, here is the Lamb of God who takes away the sin of the world!
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 This is he of whom I said, One is coming after me who is put over me because he was in existence before me.
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 I myself had no knowledge of him, but I came giving baptism with water so that he might be seen openly by Israel.
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 And John gave this witness, saying, I saw the Spirit coming down from heaven like a dove and resting on him.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 I had no knowledge who he was, but he who sent me to give baptism with water said to me, The one on whom you see the Spirit coming down and resting, it is he who gives baptism with the Holy Spirit.
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 This I saw myself and my witness is that he is the Son of God.
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 The day after, John was there again with two of his disciples;
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 And looking at Jesus while he was walking he said, See, there is the Lamb of God!
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 Hearing what he said, the two disciples went after Jesus.
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 And Jesus, turning round, saw them coming after him and said to them, What are you looking for? They said to him, Rabbi (which is to say, Master), where are you living?
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 He said to them, Come and see. They went with him then and saw where he was living; and they were with him all that day: it was then about the tenth hour of the day.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 Andrew, Simon Peter's brother, was one of the two men who, hearing what John said, went after Jesus.
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 Early in the morning he came across his brother and said to him, We have made discovery! It is the Messiah! (which is to say, the Christ).
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 And he took him to Jesus. Looking at him fixedly Jesus said, You are Simon, the son of John; your name will be Cephas (which is to say, Peter).
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 The day after this, Jesus had a desire to go into Galilee. He came across Philip and said to him, Come and be my disciple.
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 Now Philip's town was Beth-saida, where Andrew and Peter came from.
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Philip came across Nathanael and said to him, We have made a discovery! It is he of whom Moses, in the law, and the prophets were writing, Jesus of Nazareth, the son of Joseph.
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 Nazareth! said Nathanael, Is it possible for any good to come out of Nazareth? Philip said to him, Come and see.
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 Jesus saw Nathanael coming to him and said of him, See, here is a true son of Israel in whom there is nothing false.
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Nathanael said to him, Where did you get knowledge of me? In answer Jesus said, Before Philip was talking with you, while you were still under the fig-tree, I saw you.
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Nathanael said to him, Rabbi, you are the Son of God, you are King of Israel!
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 In answer Jesus said to him, You have faith because I said to you, I saw you under the fig-tree. You will see greater things than these.
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 And he said to him, Truly I say to you all, You will see heaven opening and God's angels going up and coming down on the Son of man.
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”

< John 1 >