< Job 21 >

1 Then Job made answer and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 Give attention with care to my words; and let this be your comfort.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Let me say what is in my mind, and after that, go on making sport of me.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 As for me, is my outcry against man? is it then to be wondered at if my spirit is troubled?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Take note of me and be full of wonder, put your hand on your mouth.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 At the very thought of it my flesh is shaking with fear.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Why is life given to the evil-doers? why do they become old and strong in power?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Their children are ever with them, and their offspring before their eyes.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Their houses are free from fear, and the rod of God does not come on them.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Their ox is ready at all times to give seed; their cow gives birth, without dropping her young.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 They send out their young ones like a flock, and their children have pleasure in the dance,
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 They make songs to the instruments of music, and are glad at the sound of the pipe.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Their days come to an end without trouble, and suddenly they go down to the underworld. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Though they said to God, Go away from us, for we have no desire for the knowledge of your ways.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 What is the Ruler of all, that we may give him worship? and what profit is it to us to make prayer to him?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Truly, is not their well-being in their power? (The purpose of the evil-doers is far from me.)
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 How frequently is the light of the evil-doers put out, or does trouble come on them? how frequently does his wrath take them with cords?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 How frequently are they as dry stems before the wind, or as grass taken away by the storm-wind?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 You say, God keeps punishment stored up for his children. Let him send it on the man himself, so that he may have the punishment of it!
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Let his eyes see his trouble, and let him be full of the wrath of the Ruler of all!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 For what interest has he in his house after him, when the number of his months is ended?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Is anyone able to give teaching to God? for he is the judge of those who are on high.
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 One comes to his end in complete well-being, full of peace and quiet:
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 His buckets are full of milk, and there is no loss of strength in his bones.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 And another comes to his end with a bitter soul, without ever tasting good.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Together they go down to the dust, and are covered by the worm.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 See, I am conscious of your thoughts, and of your violent purposes against me;
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 For you say, Where is the house of the ruler, and where is the tent of the evil-doer?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Have you not put the question to the travellers, and do you not take note of their experience?
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 How the evil man goes free in the day of trouble, and has salvation in the day of wrath?
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Who will make his way clear to his face? and if he has done a thing, who gives him punishment for it?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 He is taken to his last resting-place, and keeps watch over it.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 The earth of the valley covering his bones is sweet to him, and all men come after him, as there were unnumbered before him.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Why then do you give me comfort with words in which there is no profit, when you see that there is nothing in your answers but deceit?
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >