< Matthew 10 >

1 He called to himself his twelve disciples, and gave them authority over unclean spirits, to cast them out, and to heal every disease and every sickness.
Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
2 Now the names of the twelve apostles are these. The first, Simon, who is called Peter; Andrew, his brother; James the son of Zebedee; John, his brother;
Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
3 Philip; Bartholomew; Thomas; Matthew the tax collector; James the son of Alphaeus; Lebbaeus, who was also called Thaddaeus;
Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
4 Simon the Zealot; and Judas Iscariot, who also betrayed him.
Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
5 Jesus sent these twelve out and commanded them, saying, “Do not go among the Gentiles, and do not enter into any city of the Samaritans.
Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
6 Rather, go to the lost sheep of the house of Israel.
A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
7 As you go, preach, saying, ‘The Kingdom of Heaven is at hand!’
Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
8 Heal the sick, cleanse the lepers, and cast out demons. Freely you received, so freely give.
Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
9 Do not take any gold, silver, or brass in your money belts.
“Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
10 Take no bag for your journey, neither two coats, nor sandals, nor staff: for the laborer is worthy of his food.
kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
11 Into whatever city or village you enter, find out who in it is worthy, and stay there until you go on.
Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
12 As you enter into the household, greet it.
Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
13 If the household is worthy, let your peace come on it, but if it is not worthy, let your peace return to you.
In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
14 Whoever does not receive you or hear your words, as you go out of that house or that city, shake the dust off your feet.
Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
15 Most certainly I tell you, it will be more tolerable for the land of Sodom and Gomorrah in the day of judgment than for that city.
Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
16 “Behold, I send you out as sheep among wolves. Therefore be wise as serpents and harmless as doves.
“Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
17 But beware of men, for they will deliver you up to councils, and in their synagogues they will scourge you.
Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
18 Yes, and you will be brought before governors and kings for my sake, for a testimony to them and to the nations.
Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
19 But when they deliver you up, do not be anxious how or what you will say, for it will be given you in that hour what you will say.
Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
20 For it is not you who speak, but the Spirit of your Father who speaks in you.
gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
21 “Brother will deliver up brother to death, and the father his child. Children will rise up against parents and cause them to be put to death.
“Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
22 You will be hated by all men for my name’s sake, but he who endures to the end will be saved.
Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
23 But when they persecute you in this city, flee into the next, for most certainly I tell you, you will not have gone through the cities of Israel until the Son of Man has come.
Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
24 “A disciple is not above his teacher, nor a servant above his lord.
“Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
25 It is enough for the disciple that he be like his teacher, and the servant like his lord. If they have called the master of the house Beelzebul, how much more those of his household!
Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
26 Therefore do not be afraid of them, for there is nothing covered that will not be revealed, or hidden that will not be known.
“Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
27 What I tell you in the darkness, speak in the light; and what you hear whispered in the ear, proclaim on the housetops.
Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
28 Do not be afraid of those who kill the body, but are not able to kill the soul. Rather, fear him who is able to destroy both soul and body in Gehenna (Geenna g1067).
Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
29 “Are not two sparrows sold for an assarion coin? Not one of them falls to the ground apart from your Father’s will.
Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
30 But the very hairs of your head are all numbered.
Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
31 Therefore do not be afraid. You are of more value than many sparrows.
Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
32 Everyone therefore who confesses me before men, I will also confess him before my Father who is in heaven.
“Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
33 But whoever denies me before men, I will also deny him before my Father who is in heaven.
Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
34 “Do not think that I came to send peace on the earth. I did not come to send peace, but a sword.
“Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
35 For I came to set a man at odds against his father, and a daughter against her mother, and a daughter-in-law against her mother-in-law.
Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
36 A man’s foes will be those of his own household.
abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
37 He who loves father or mother more than me is not worthy of me; and he who loves son or daughter more than me is not worthy of me.
“Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
38 He who does not take his cross and follow after me is not worthy of me.
duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
39 He who seeks his life will lose it; and he who loses his life for my sake will find it.
Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
40 “He who receives you receives me, and he who receives me receives him who sent me.
“Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
41 He who receives a prophet in the name of a prophet will receive a prophet’s reward. He who receives a righteous man in the name of a righteous man will receive a righteous man’s reward.
Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
42 Whoever gives one of these little ones just a cup of cold water to drink in the name of a disciple, most certainly I tell you, he will in no way lose his reward.”
In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”

< Matthew 10 >