< Mark 11 >

1 When they came near to Jerusalem, to Bethsphage and Bethany, at the Mount of Olives, he sent two of his disciples
Da suka kusa Urushalima, kusa da Betafaji, da Betanya, wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu
2 and said to them, “Go your way into the village that is opposite you. Immediately as you enter into it, you will find a young donkey tied, on which no one has sat. Untie him and bring him.
ya ce masu, “ku shiga kauyen can kusa da mu. Da zarar kun shiga za ku ga aholaki a daure, wanda ba a taba hawa ba. Ku kwance shi, ku kawo mani.
3 If anyone asks you, ‘Why are you doing this?’ say, ‘The Lord needs him;’ and immediately he will send him back here.”
In wani ya ce maku, “Don me kuke haka? ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsa, zai kuma komo da shi nan da nan.”'
4 They went away, and found a young donkey tied at the door outside in the open street, and they untied him.
Sai suka tafi, suka tadda aholakin a daure a kofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.
5 Some of those who stood there asked them, “What are you doing, untying the young donkey?”
sai wadanda suke tsaye a gun suka ce masu, “Don me kuke kwance aholakin nan?
6 They said to them just as Jesus had said, and they let them go.
Suka fada masu abinda Yesu yace, sai suka kyale su suka tafi.
7 They brought the young donkey to Jesus and threw their garments on it, and Jesus sat on it.
Almajiran nan biyu suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfida mayafansu a kai, sai ya hau.
8 Many spread their garments on the way, and others were cutting down branches from the trees and spreading them on the road.
Sai mutane da yawa suka shimfida mayafansu a hanya, wadansu kuma suka baza ganyen da suka yanko daga filayen.
9 Those who went in front and those who followed cried out, “Hosanna! Blessed is he who comes in the name of the Lord!
Wadanda suke gaba da shi da wadanda ke bin bayansa suka yi sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji.
10 Blessed is the kingdom of our father David that is coming in the name of the Lord! Hosanna in the highest!”
Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na Ubanmu Dawuda! Dukaka a cikin sama!”
11 Jesus entered into the temple in Jerusalem. When he had looked around at everything, it being now evening, he went out to Bethany with the twelve.
San nan Yesu ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Sai ya dudduba komai, da magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyu nan.
12 The next day, when they had come out from Bethany, he was hungry.
Kashe gari, suka tashi daga Betanya, sai ya ji yunwa.
13 Seeing a fig tree afar off having leaves, he came to see if perhaps he might find anything on it. When he came to it, he found nothing but leaves, for it was not the season for figs.
Da ya hango itacen baure mai ganye daga nesa sai ya je ya ga ko za sami 'ya'ya. Da ya iso wurinsa bai ga komai ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan baure ba ne.
14 Jesus told it, "May no one eat fruit from you again for the age (aiōn g165)!" And his disciples heard it.
Sai ya ce wa bauren, “Kada kowa ya kara cin ''ya'yanka har abada!” Almajiransa kuwa sun ji maganar. (aiōn g165)
15 They came to Jerusalem, and Jesus entered into the temple and began to throw out those who sold and those who bought in the temple, and overthrew the money changers’ tables and the seats of those who sold the doves.
Suka iso Urushalima, da shigar su, ya kori masu saye da sayarwa, ya watsar da taburan 'yan canjin kudi, da kujerun masu sayar da tantabaru.
16 He would not allow anyone to carry a container through the temple.
Ya hana kowa ya dauki wani abu da za a i ya sayarwa a cikin haikalin.
17 He taught, saying to them, “Is not it written, ‘My house will be called a house of prayer for all the nations’? But you have made it a den of robbers!”
Sai ya koyar da su cewa, “Ashe ba rubuce yake ba, “Za a kira gidana gidan addu'a na dukan al'ummai? Amma ku kun mayar da shi kogon yan fashi”.
18 The chief priests and the scribes heard it, and sought how they might destroy him. For they feared him, because all the multitude was astonished at his teaching.
Da mayan Faristoci da marubutan attaura suka ji maganar da ya yi, sai suka nami hanyar da za su kashe shi. Amma suka ji tsoronsa domin dukkan taron na mamakin koyarwarsa.
19 When evening came, he went out of the city.
Kowace yamma kuma, sukan fita gari.
20 As they passed by in the morning, they saw the fig tree withered away from the roots.
Da safe suna wucewa, sai suka ga bauren nan ya bushe.
21 Peter, remembering, said to him, “Rabbi, look! The fig tree which you cursed has withered away.”
Bitrus kuwa ya tuna ya ce “Malam, dubi! Baurenan da ka la'anta ya bushe.”
22 Jesus answered them, “Have faith in God.
Yesu ya amsa masu ya ce, “ku gaskata da Allah.”
23 For most certainly I tell you, whoever may tell this mountain, ‘Be taken up and cast into the sea,’ and does not doubt in his heart, but believes that what he says is happening, he shall have whatever he says.
Hakika, ina gaya maku, duk wanda ya ce wa dutsen nan tashi ka fada cikin tekun', bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata haka kuwa zai faru, haka kuwa Allah zai yi.
24 Therefore I tell you, all things whatever you pray and ask for, believe that you have received them, and you shall have them.
Saboda haka ina dai gaya maku, komai kuka yi addu'a kuka roka, ku gaskata cewa samamme ne, zai kuma zama naku.
25 Whenever you stand praying, forgive, if you have anything against anyone; so that your Father, who is in heaven, may also forgive you your transgressions.
Duk sa'add da kuke addu'a ku gafarta wa wadanda suka yi maku laifi, domin Ubanku shima zai gafarta maku naku laifi.”
26 But if you do not forgive, neither will your Father in heaven forgive your transgressions.”
(Amma in baku gafartawa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma da ke sama ba zai gafarta maku ba.)
27 They came again to Jerusalem, and as he was walking in the temple, the chief priests, the scribes, and the elders came to him,
Da suka sake dawowa Urushalima. Yasu na tafiya cikin haikali, sai manyan firistoci, da marubuta, da dattawa suka zo wurinsa,
28 and they began saying to him, “By what authority do you do these things? Or who gave you this authority to do these things?”
suka ce masa, “Da wanne iko kake yin wadanan abubuwa? Ko kuwa wa ya ba ka ikon yinsu? “
29 Jesus said to them, “I will ask you one question. Answer me, and I will tell you by what authority I do these things.
Sai Yesu ya ce masu, “Zan yi maku wata tambaya. ku ba ni amsa, ni kuwa zan gaya maku ko da wanne iko ne nake yin wadannan abubuwan.
30 The baptism of John—was it from heaven, or from men? Answer me.”
Baftismar da Yahaya yayi, daga sama take ko kuwa daga mutum take? ku bani amsa”.
31 They reasoned with themselves, saying, “If we should say, ‘From heaven;’ he will say, ‘Why then did you not believe him?’
Sai suka yi mahuwara da juna, suka ce, “in kuwa muka ce, 'daga sama take,' za ya ce, “To, don me ba ku gaskata shi ba?
32 If we should say, ‘From men’”—they feared the people, for all held John to really be a prophet.
In kuwa muka ce, “amma in muka ce ta mutum ce zasu jejjefemu domi suna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne.
33 They answered Jesus, “We do not know.” Jesus said to them, “Neither will I tell you by what authority I do these things.”
Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba” Yesu ya ce masu, “Haka ni kuma ba zan fada muku ko da wanne iko nake yin abubuwan nan ba.”

< Mark 11 >