< John 16 >

1 “I have said these things to you so that you would not be caused to stumble.
“Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube.
2 They will put you out of the synagogues. Yes, the time is coming that whoever kills you will think that he offers service to God.
Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.
3 They will do these things because they have not known the Father nor me.
Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba.
4 But I have told you these things so that when the time comes, you may remember that I told you about them. I did not tell you these things from the beginning, because I was with you.
Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku.” Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.
5 But now I am going to him who sent me, and none of you asks me, ‘Where are you going?’
Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?'
6 But because I have told you these things, sorrow has filled your heart.
Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku.
7 Nevertheless I tell you the truth: It is to your advantage that I go away; for if I do not go away, the Counselor will not come to you. But if I go, I will send him to you.
Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 When he has come, he will convict the world about sin, about righteousness, and about judgment;
Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci.
9 about sin, because they do not believe in me;
Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba,
10 about righteousness, because I am going to my Father, and you will not see me any more;
Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba,
11 about judgment, because the prince of this world has been judged.
game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.
12 “I still have many things to tell you, but you cannot bear them now.
“Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba.
13 However, when he, the Spirit of truth, has come, he will guide you into all truth, for he will not speak from himself; but whatever he hears, he will speak. He will declare to you things that are coming.
Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru.
14 He will glorify me, for he will take from what is mine and will declare it to you.
Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.
15 All things that the Father has are mine; therefore I said that he takes of mine and will declare it to you.
Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku.
16 “A little while, and you will not see me. Again a little while, and you will see me.”
“Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni.”
17 Some of his disciples therefore said to one another, “What is this that he says to us, ‘A little while, and you will not see me, and again a little while, and you will see me;’ and, ‘Because I go to the Father’?”
Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, “Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?”
18 They said therefore, “What is this that he says, ‘A little while’? We do not know what he is saying.”
Saboda haka sukace, “Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba.”
19 Therefore Jesus perceived that they wanted to ask him, and he said to them, “Do you inquire among yourselves concerning this, that I said, ‘A little while, and you will not see me, and again a little while, and you will see me’?
Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, “Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, “Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'?
20 Most certainly I tell you that you will weep and lament, but the world will rejoice. You will be sorrowful, but your sorrow will be turned into joy.
Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki.
21 A woman, when she gives birth, has sorrow because her time has come. But when she has delivered the child, she does not remember the anguish any more, for the joy that a human being is born into the world.
Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.
22 Therefore you now have sorrow, but I will see you again, and your heart will rejoice, and no one will take your joy away from you.
To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki.
23 “In that day you will ask me no questions. Most certainly I tell you, whatever you may ask of the Father in my name, he will give it to you.
A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi.
24 Until now, you have asked nothing in my name. Ask, and you will receive, that your joy may be made full.
Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke.”
25 “I have spoken these things to you in figures of speech. But the time is coming when I will no more speak to you in figures of speech, but will tell you plainly about the Father.
“Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.
26 In that day you will ask in my name; and I do not say to you that I will pray to the Father for you,
A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba,
27 for the Father himself loves you, because you have loved me, and have believed that I came from God.
domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito.
28 I came from the Father and have come into the world. Again, I leave the world and go to the Father.”
Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 His disciples said to him, “Behold, now you are speaking plainly, and using no figures of speech.
Almajiransa sukace, duba, “Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba!
30 Now we know that you know all things, and do not need for anyone to question you. By this we believe that you came from God.”
Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.”
31 Jesus answered them, “Do you now believe?
Yesu ya amsa masu yace, “Ashe, yanzu kun gaskata?
32 Behold, the time is coming, yes, and has now come, that you will be scattered, everyone to his own place, and you will leave me alone. Yet I am not alone, because the Father is with me.
Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni.
33 I have told you these things, that in me you may have peace. In the world you have trouble; but cheer up! I have overcome the world.”
Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,”

< John 16 >