< John 16 >

1 “I have said these things to you so that you would not be caused to stumble.
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
2 They will put you out of the synagogues. Yes, the time is coming that whoever kills you will think that he offers service to God.
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
3 They will do these things because they have not known the Father nor me.
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
4 But I have told you these things so that when the time comes, you may remember that I told you about them. I did not tell you these things from the beginning, because I was with you.
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
5 But now I am going to him who sent me, and none of you asks me, ‘Where are you going?’
“Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
6 But because I have told you these things, sorrow has filled your heart.
Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
7 Nevertheless I tell you the truth: It is to your advantage that I go away; for if I do not go away, the Counselor will not come to you. But if I go, I will send him to you.
Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 When he has come, he will convict the world about sin, about righteousness, and about judgment;
Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
9 about sin, because they do not believe in me;
a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
10 about righteousness, because I am going to my Father, and you will not see me any more;
a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
11 about judgment, because the prince of this world has been judged.
a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
12 “I still have many things to tell you, but you cannot bear them now.
“Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
13 However, when he, the Spirit of truth, has come, he will guide you into all truth, for he will not speak from himself; but whatever he hears, he will speak. He will declare to you things that are coming.
Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
14 He will glorify me, for he will take from what is mine and will declare it to you.
Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
15 All things that the Father has are mine; therefore I said that he takes of mine and will declare it to you.
Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
16 “A little while, and you will not see me. Again a little while, and you will see me.”
Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
17 Some of his disciples therefore said to one another, “What is this that he says to us, ‘A little while, and you will not see me, and again a little while, and you will see me;’ and, ‘Because I go to the Father’?”
A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
18 They said therefore, “What is this that he says, ‘A little while’? We do not know what he is saying.”
Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
19 Therefore Jesus perceived that they wanted to ask him, and he said to them, “Do you inquire among yourselves concerning this, that I said, ‘A little while, and you will not see me, and again a little while, and you will see me’?
Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
20 Most certainly I tell you that you will weep and lament, but the world will rejoice. You will be sorrowful, but your sorrow will be turned into joy.
Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
21 A woman, when she gives birth, has sorrow because her time has come. But when she has delivered the child, she does not remember the anguish any more, for the joy that a human being is born into the world.
Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
22 Therefore you now have sorrow, but I will see you again, and your heart will rejoice, and no one will take your joy away from you.
Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
23 “In that day you will ask me no questions. Most certainly I tell you, whatever you may ask of the Father in my name, he will give it to you.
A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
24 Until now, you have asked nothing in my name. Ask, and you will receive, that your joy may be made full.
Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
25 “I have spoken these things to you in figures of speech. But the time is coming when I will no more speak to you in figures of speech, but will tell you plainly about the Father.
“Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
26 In that day you will ask in my name; and I do not say to you that I will pray to the Father for you,
A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
27 for the Father himself loves you, because you have loved me, and have believed that I came from God.
Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
28 I came from the Father and have come into the world. Again, I leave the world and go to the Father.”
Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 His disciples said to him, “Behold, now you are speaking plainly, and using no figures of speech.
Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
30 Now we know that you know all things, and do not need for anyone to question you. By this we believe that you came from God.”
Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
31 Jesus answered them, “Do you now believe?
Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
32 Behold, the time is coming, yes, and has now come, that you will be scattered, everyone to his own place, and you will leave me alone. Yet I am not alone, because the Father is with me.
Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
33 I have told you these things, that in me you may have peace. In the world you have trouble; but cheer up! I have overcome the world.”
“Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”

< John 16 >