< Numbers 24 >

1 And when Balaam saw that it pleased Jehovah to bless Israel, he did not go, as at the other times, to meet with omens, but he set his face toward the wilderness.
To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
2 And Balaam lifted up his eyes, and he saw Israel dwelling according to their tribes, and the Spirit of God came upon him.
Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
3 And he took up his oracle, and said, Balaam the son of Beor says, and the man whose eye was closed says,
sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
4 he says who hears the words of God, who sees the vision of the Almighty, falling down, and having his eyes open,
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
5 How goodly are thy tents, O Jacob, thy tabernacles, O Israel!
“Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
6 As valleys they are spread forth, as gardens by the river-side, as aloes which Jehovah has planted, as cedar trees beside the waters.
“Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
7 Water shall flow from his buckets, and his seed shall be in many waters, and his king shall be higher than Agag, and his kingdom shall be exalted.
Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
8 God brings him forth out of Egypt. He has as it were the strength of the wild-ox. He shall eat up the nations his adversaries, and shall break their bones in pieces, and smite them through with his arrows.
“Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
9 He couched, he lay down as a lion, and as a lioness. Who shall rouse him up? He who blesses thee is blessed, And he who curses thee is cursed.
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
10 And Balak's anger was kindled against Balaam, and he struck his hands together. And Balak said to Balaam, I called thee to curse my enemies, and, behold, thou have altogether blessed them these three times.
Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
11 Therefore now flee thou to thy place. I thought to promote thee to great honor, but, lo, Jehovah has kept thee back from honor.
Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
12 And Balaam said to Balak, Did I not also speak to thy messengers that thou sent to me, saying,
Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
13 If Balak would give me his house full of silver and gold, I cannot go beyond the word of Jehovah, to do either good or bad of my own mind. What Jehovah speaks, that I will speak?
‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
14 And now, behold, I go to my people. Come, I will advise thee what this people shall do to thy people in the latter days.
Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
15 And he took up his oracle, and said, Balaam the son of Beor says, and the man whose eye was closed says,
Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
16 he says who hears the words of God, and knows the knowledge of the Most High, who sees the vision of the Almighty, falling down, and having his eyes open:
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
17 I see him, but not now. I behold him, but not near. There shall come forth a star out of Jacob, and a scepter shall rise out of Israel, and shall smite through the corners of Moab, and break down all the sons of tumult.
“Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
18 And Edom shall be a possession, Seir also shall be a possession, who were his enemies, while Israel does valiantly.
Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
19 And out of Jacob shall come he who shall have dominion, and shall destroy the remnant from the city.
Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
20 And he looked on Amalek, and took up his oracle, and said, Amalek was the first of the nations, but his latter end shall come to destruction.
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21 And he looked on the Kenite, and took up his oracle, and said, Strong is thy dwelling-place, and thy nest is set in the rock.
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22 Nevertheless Kain shall be wasted, until Asshur shall carry thee away captive.
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23 And he took up his oracle, and said, Alas, who shall live when God does this?
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24 But ships shall come from the coast of Kittim, and they shall afflict Asshur, and shall afflict Eber, and he also shall come to destruction.
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25 And Balaam rose up, and went and returned to his place, and Balak also went his way.
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

< Numbers 24 >