< Zakarias 13 >

1 På hin Dag skal en Kilde vælde frem for Davids Hus og Jerusalems Indbyggere mod Synd og Urenhed.
“A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
2 Og på hin bag, lyder det fra Hærskarers HERRE, udrydder jeg Afgudernes Navne af Landet, så de ikke mer skal ihukommes; også Profeterne og Urenhedens Ånd driver jeg ud af Landet.
“A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
3 Når nogen da atter profeterer, skal hans egne Forældre, hans Fader og Moder, sige til ham: Du har forbrudt dit Liv, thi du har talt Løgn i HERRENs Navn." Og hans egne Forældre, hans Fader og Moder, skal gennembore ham, når han profeterer.
In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
4 På hin Dag skal hver en Profet skamme sig over sine Syner, når han profeterer, og han skal ikke klæde sig i lådden Kappe for at føre Folk bag Lyset,
“A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
5 men sige: "Jeg er ingen Profet; jeg er Bonde og har dyrket Jord fra min Ungdom."
Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
6 Og spørger man ham: "Hvad er det for Sår på dit Bryst?" skal han sige: "Dem fik jeg i mine Boleres Hus."
In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
7 Frem, Sværd, imod min Hyrde, mod Manden, som står mig nær, så lyder det fra Hærskarers HERRE. Hyrden vil jeg slå, så Fårehjorden spredes; mod Drengene løfter jeg Hånden.
“Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
8 Og i hele Landet lyder det fra HERREN, skal to Tredjedele udryddes og udånde, men een Tredjedel skal levnes.
A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
9 Og denne Tredjedel fører jeg i Ild og renser den, som man renser Sølv, prøver den, som man prøver Guld. Den skal påkalde mit Navn, og jeg svarer; jeg siger: "Den er mit Folk." Og den skal sige: "HERREN er min Gud."
Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”

< Zakarias 13 >