< 1 Mosebog 9 >

1 Derpå velsignede Gud Noa og hans Sønner og sagde til dem: Bliv frugtbare og mangfoldige og opfyld Jorden!
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 Frygt for eder og Rædsel for eder skal være over alle Jordens vildtlevende Dyr og alle Himmelens Fugle og i alt, hvad Jorden vrimler med, og i alle Havets Fisk; i eders Hånd er de givet!
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Alt, hvad der rører sig og lever, skal tjene eder til Føde; ligesom de grønne Urter giver jeg eder det alt sammen.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Dog Kød med Sjælen, det er Blodet, må I ikke spise!
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 Men for eders eget Blod kræver jeg Hævn; af ethvert Dyr kræver jeg Hævn for det, og af Menneskene indbyrdes kræver jeg Hævn for Menneskenes Liv.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Om nogen udøser Menneskers Blod, ved Mennesker skal hans Blod udøses, thi i sit Billede gjorde Gud Menneskene.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 Men I skal blive frugtbare og mangfoldige! Opfyld Jorden og gør eder til Herre over den!"
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 Derpå sagde Gud til Noa og hans Sønner:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 "Se, jeg opretter min Pagt med eder og eders Efterkommere efter eder
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 og med hvert levende Væsen, som er hos eder, Fuglene, Kvæget og alle Jordens vildtlevende Dyr, alt, hvad der gik ud af Arken, alle Jordens Dyr;
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 jeg opretter min Pagt med eder og lover, at aldrig mere skal alt Kød udryddes af Flodens Vande, og aldrig mere skal der komme en Vandflod for at ødelægge Jorden!"
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Fremdeles sagde Gud: "Dette er Tegnet på den Pagt, jeg til evige Tider opretter mellem mig og eder og hvert levende Væsen, som er hos eder:
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 Min Bue sætter jeg i Skyen, og den skal være Pagtstegn mellem mig og Jorden!
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Når jeg trækker Skyer sammen over Jorden, og Buen da viser sig i Skyerne,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 vil jeg komme den Pagt i Hu, som består mellem mig og eder og hvert levende Væsen, det er alt Kød, og Vandet skal ikke mere blive til en Vandflod, som ødelægger alt Kød.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 Når Buen da står i Skyerne, vil jeg se hen til den og ihukomme den evige Pagt mellem Gud og hvert levende Væsen, det er alt Kød på Jorden."
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Og Gud sagde til Noa: "Det er Tegnet på den Pagt, jeg opretter imellem mig og alt Kød på Jorden!"
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 Noas Sønner, der gik ud af Arken, var Sem, Kam og Jafet; Kam var Fader til Kana'an;
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 det var Noas tre Sønner, og fra dem stammer hele Jordens Befolkning.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 Noa var Agerdyrker og den første, der plantede en Vingård.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 Da han nu drak af Vinen, blev han beruset og blottede sig inde i, sit Telt.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 Da så Kana'ans Fader Kam sin Faders Blusel og gik ud og fortalte sine Brødre det;
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 men Sem og Jafet tog Kappen, lagde den på deres Skuldre og gik baglæns ind og tildækkede deres Faders Blusel med bortvendte Ansigter, så de ikke så deres Faders Blusel.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Da Noa vågnede af sin Rus og fik at vide, hvad hans yngste Søn havde gjort ved ham,
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 sagde han: "Forbandet være Kana'an, Trælles Træl blive han for sine Brødre!"
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Fremdeles sagde han: "Lovet være HERREN, Sems Gud, og Kana'an blive hans Træl!
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Gud skaffe Jafet Plads, at han må bo i Sems Telte; og Kana'an blive hans Træl!"
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 Noa levede 350 År efter Vandfloden;
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 således blev Noas fulde Levetid 950 År, og derpå døde han.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.

< 1 Mosebog 9 >