< Ezekiel 4 >

1 Du Mennneskesøn tag dig en teglsten, læg den for dig og indrids i den et Billede af en By, Jerusalem;
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
2 og kast en Vold op omkring den, byg Belejringstårne, opkast Stormvold, lad Hære lejre sig imod den og rejs Stormbukke mod den fra alle Sider;
Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
3 tag dig så en Jernpande og sæt den som en Jernvæg op mellem dig og Byen og ret dit Ansigt imod den. Således skal den være omringet, og du skal trænge den. Det skal være Israels Hus et Tegn.
Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
4 Og læg du dig på din venstre Side og tag, Israels Huss Misgerning på dig; alle de Dage du ligger således, skal du bære deres Misgerning.
“Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
5 Deres Misgernings År gør jeg til lige så mange Dage for dig, 190 Dage; så længe skal du bære Israels Huss Misgerning.
Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
6 Og når de er til Ende, læg dig så på din højre Side og bær Judas Huss Misgerning 40 Dage; for hvert År giver jeg dig en Dag.
“Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
7 Og du skal rette dit Ansigt og din blottede Arm mod det omringede Jerusalem og profetere imod det.
Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
8 Og se, jeg lægger Bånd på dig, så du ikke kan vende dig fra den ene Side til den anden, før din Belejrings Dage er til Ende.
Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
9 Og tag du dig Hvede, Byg, Bønner, Linser, Hirse og Spelt, kom det i et og samme Kar og lav dig Brød deraf; alle de Dage du ligger på Siden, 190 Dage, skal det være din Mad;
“Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
10 og Maden, du får, skal være efter Vægt, tyve Sekel daglig; du skal spise den een Gang daglig.
Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
11 Og Vand skal du drikke efter Mål, en Sjettedel Hin; du skal drikke een Gang daglig.
Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
12 Og som Bygkager skal du spise det og bage det ved Menneskeskarn i deres Påsyn.
Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
13 Og du skal sige: "Så sige HERREN: Således skal Israeliterne have urent Brød til Føde blandt de Folk, jeg bortstøder dem til!"
Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
14 Men jeg sagde: "Ak, Herre, HERRE, jeg har endnu aldrig været uren; noget selvdødt eller sønderrevet har jeg fra Barnsben aldrig spist, og urent Kød kom aldrig i min Mund!"
Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
15 Da svarede han: "Vel, jeg tillader dig at tage Oksegødning i Stedet for Menneskeskarn og bage dit Brød derved."
Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
16 Videre sagde han til mig: Menneskesøn! Se, jeg bryder Brødets Støttestav i Jerusalem; Brød skal de spise efter Vægt og i Angst, og Vand skal de drikke efter Mål og i Rædsel,
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
17 for at de må mangle Brød og Vand og alle som een være slagne af Rædsel og hensmægte i deres Misgerning.
domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.

< Ezekiel 4 >