< 诗篇 29 >

1 大卫的诗。 神的众子啊,你们要将荣耀、能力归给耶和华, 归给耶和华!
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 要将耶和华的名所当得的荣耀归给他, 以圣洁的妆饰敬拜耶和华。
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 耶和华的声音发在水上; 荣耀的 神打雷, 耶和华打雷在大水之上。
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 耶和华的声音大有能力; 耶和华的声音满有威严。
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 耶和华的声音震破香柏树; 耶和华震碎黎巴嫩的香柏树。
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 他也使之跳跃如牛犊, 使黎巴嫩和西连跳跃如野牛犊。
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 耶和华的声音使火焰分岔。
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 耶和华的声音震动旷野; 耶和华震动加低斯的旷野。
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 耶和华的声音惊动母鹿落胎, 树木也脱落净光。 凡在他殿中的,都称说他的荣耀。
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 洪水泛滥之时,耶和华坐着为王; 耶和华坐着为王,直到永远。
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 耶和华必赐力量给他的百姓; 耶和华必赐平安的福给他的百姓。
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< 诗篇 29 >