< ᎣᏍᏛ ᎧᏃᎮᏛ ᎹᎦ ᎤᏬᏪᎳᏅᎯ 10 >

1 ᎾᎿᎭᏃ ᏚᎴᏅ, ᏧᏗᏱ ᎦᏓ ᎠᎲᎢ ᎤᎷᏤᎢ, ᏦᏓᏂ ᎠᏍᎪᏂᏗᏢ ᏧᎶᎯᏍᏔᏁᎢ; ᎠᎴ ᎤᏂᏣᏘ ᏴᏫ ᏔᎵᏁ ᎢᎬᏩᏓᏟᏌᏁᎴᎢ; ᎠᎴ ᎢᏳᏛᏁᏗ ᎨᏒ ᏄᏛᏁᎴᎢ, ᏔᎵᏁ ᏚᏪᏲᏁᎢ.
Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
2 ᎠᏂᏆᎵᏏᏃ ᎬᏩᎷᏤᎸ ᎬᏩᏛᏛᏁᎢ, ᎯᎠ ᏄᏂᏪᏎᎢ, ᏚᏳᎪᏗᏍᎪ ᎠᏍᎦᏯ ᎤᏓᎢᏅᏗᏱ ᎤᏓᎵᎢ? ᎬᏩᎪᎵᏰᏍᎨᎢ.
Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
3 ᎤᏁᏨᏃ ᎯᎠ ᏂᏑᏪᏎᎴᎢ, ᎦᏙ ᎤᏍᏕ ᎢᏥᏁᏤᎴ ᎼᏏ?
Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 ᎯᎠᏃ ᏄᏂᏪᏎᎢ, ᎼᏏ ᎤᎵᏍᎪᎸᏔᏁ ᎪᏪᎶᏗᏱ ᏙᎦᎴᏅᎲᎢ, ᎠᎴ ᎠᏓᎢᏅᏗᏱ.
Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
5 ᏥᏌᏃ ᎤᏁᏨ, ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᏗᏍᏓᏱᏳ ᎨᏒ ᎢᏳᏍᏗ ᏗᏥᎾᏫ ᎯᎠ ᎾᏍᎩ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᎢᏦᏪᎳᏁᎴᎢ;
Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
6 ᏗᏓᎴᏂᏍᎬᏍᎩᏂ ᎤᏪᏢᏅᏅᎢ, ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎠᏍᎦᏯ ᎠᎴ ᎠᎨᏴ ᏚᏬᏢᏁᎢ.
Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
7 ᎾᏍᎩ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᏍᎦᏯ ᏕᎬᏕᎨᏍᏗ ᎤᏙᏓ ᎠᎴ ᎤᏥ, ᎠᎴ ᎤᏓᎵᎢ ᎠᏜᏓᏩᏍᏗᏍᎨᏍᏗ;
‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
8 ᎾᏍᎩᏃ ᎠᏂᏔᎵ ᏌᏉᏉ ᎨᏎᏍᏗ ᎤᏂᏇᏓᎸᎢ; ᎾᏍᎩᏃ ᎥᏝ ᎿᎭᏉ ᎠᏂᏔᎵ ᏱᎩ, ᏌᏉᏉᏍᎩᏂ ᎤᏂᏇᏓᎸᎢ.
su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
9 ᎾᏍᎩ ᎢᏳᏍᏗ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᏧᏭᏓᏔᏅᎯ ᏞᏍᏗ ᏴᏫ ᏧᎦᎴᏅᏔᏅᎩ.
Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
10 ᎦᎵᏦᏕᏃ ᎠᏂᏯᎥ ᎬᏩᏍᏓᏩᏗᏙᎯ ᏔᎵᏁ ᎢᎬᏩᏛᏛᏁ ᎾᏍᎩ ᎤᎬᏩᎵ.
Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
11 ᎯᎠᏃ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᎩᎶ ᎤᏓᎵᎢ ᎠᏓᎡᎨᏍᏗ, ᎠᎴ ᏅᏩᏓᎴ ᎠᏓᏰᎨᏍᏗ, ᎾᏍᎩ ᎠᏓᏲᏁᎮᏍᏗ ᎠᏍᎦᏅᏤᎮᏍᏗ ᎾᏍᎩ.
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
12 ᎢᏳ ᎠᎴ ᎠᎨᏴ ᎤᏰᎯ ᎠᏓᎡᎨᏍᏗ, ᎠᎴ ᏅᏩᏓᎴ ᏓᎾᏤᎨᏍᏗ, ᎾᏍᎩ ᎠᏓᏲᏁᎮᏍᏗ.
In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
13 ᏧᎾᏍᏗᏃ ᏗᏂᏲᎵ ᏕᎬᏩᏘᏃᎮᎴᎢ, ᎾᏍᎩ ᏧᏒᏂᏍᏗᏱ; ᎬᏩᏍᏓᏩᏗᏙᎯᏃ ᏚᏂᎬᏍᎪᎸᏁ ᎾᏍᎩ ᏧᎾᏘᏃᎸᎯ.
Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
14 ᏥᏌᏍᎩᏂ ᎤᎪᎲ ᎤᏣᏘ ᏒᏍᎦ ᎤᏰᎸᏁᎢ, ᎠᎴ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᎤᏁᎳᎩ ᏕᏤᎵᏎᎮᏍᏗ ᏧᎾᏍᏗ ᏗᏂᏲᎵ ᎬᎩᎷᏤᏗᏱ, ᎠᎴ ᏞᏍᏗ ᏱᏗᏥᏅᏍᏓᏕᎮᏍᏗ; ᎾᏍᎩᏰᏃ ᏄᎾᏍᏗ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏤᎵᎪᎯ.
Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
15 ᎤᏙᎯᏳᎯᏯ ᎯᎠ ᏂᏨᏪᏎᎭ, ᎢᏳᏃ ᎩᎶ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᎬᏫᏳᎯ ᎨᏒ ᏂᏓᏓᏂᎸᎬᎾ ᎢᎨᏎᏍᏗ ᎾᏍᎩᏯ ᎠᏲᎵ ᏥᏓᏓᏂᎸᎪᎢ, ᎥᏝ ᎾᎿᎭᏱᏮᎬᏴᎭ.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
16 ᏚᏁᏒᏃ ᎠᎴ ᏚᏏᏔᏛ, ᎣᏍᏛ ᏚᏁᏤᎴᎢ.
Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
17 ᎤᏂᎩᏒᏃ ᎦᏅᏅ ᏭᎷᏨ, ᎩᎶ ᎢᏳᏍᏗ ᎤᏗᏠᎡᎸᎩ, ᎠᎴ ᏚᎵᏂᏆᏅᏁᎸᎩ, ᎤᏛᏛᏁ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᎰᏍᏛ ᏔᏕᏲᎲᏍᎩ, ᎦᏙ ᏓᎦᏛᏁᎵ ᎤᎵᏍᏆᏗᏍᏗ ᏂᎨᏒᎾ ᎬᏂᏛ ᎠᏆᏤᎵ ᎢᏳᎵᏍᏙᏗᏱ? (aiōnios g166)
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
18 ᏥᏌᏃ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᎦᏙᏃ ᎰᏍᏛ ᎢᏍᏉᏎᎭ ᎠᏴ? ᎥᏝ ᎩᎶ ᎣᏍᏛ ᏱᎩ, ᏌᏉ ᎤᏩᏒᎯᏳ, ᎾᏍᎩ ᎤᏁᎳᏅᎯ.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
19 ᏕᎯᎦᏔᎭ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ, ᎾᏍᎩ, ᏞᏍᏗ ᏣᏓᏲᏁᎸᎩ, ᏞᏍᏗ ᏣᏓᎸᎩ, ᏞᏍᏗ ᏣᏃᏍᎩᏒᎩ, ᏞᏍᏗ ᎦᏰᎪᎩ ᏣᏃᎮᎸᎩ, ᏞᏍᏗ ᏣᏓᎶᏄᎮᎸᎩ, ᏣᏙᏓ ᎠᎴ ᏣᏥ ᏕᎯᎸᏉᏕᏍᏗ.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
20 ᎤᏁᏨᏃ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᏔᏕᏲᎲᏍᎩ, ᎯᎠ ᎾᏍᎩ ᏂᎦᏛ ᏓᎩᏍᏆᏂᎪᏔᏅ ᏥᏧᏣ ᎨᏒ ᏅᏓᎬᏩᏓᎴᏅᏛ.
Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
21 ᏥᏌᏃ ᏚᎧᎿᎭᏅ, ᎤᎨᏳᎯᏳ ᏄᎵᏍᏔᏁᎢ, ᎠᎴ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᏑᏓᎴᎩ ᏣᎷᎳ; ᎮᎾ ᏫᎾᏚᎦ ᏂᎦᎥ ᎪᎱᏍᏗ ᏣᎾᎥᎢ, ᎠᎴ ᎤᏲ ᎢᏳᎾᏛᎿᎭᏕᎩ ᎩᏁᎸᎭ, ᏦᏒᏃ ᏫᏣᎮᏍᏗ ᏧᎬᏩᎶᏗ; ᎠᎴ ᏖᏒᎭ, ᏧᏓᎿᎭᏩᏛ ᎯᏴᎲᎭ, ᎠᎴ ᏍᎩᏍᏓᏩᏕᏒᎭ.
Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
22 ᎤᏲᏃ ᎤᏰᎸᏁ ᎾᏍᎩ ᎾᏥᏪᏎᎸ, ᎠᎴ ᎡᎯᏍᏗ ᎬᏩᏓᏅᏘ ᎤᏓᏅᏎᎢ; ᎤᏣᏘᏰᏃ ᎤᎿᎭᎡᎢ.
Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
23 ᏥᏌᏃ ᎤᏚᏫᏛ ᏚᎧᎿᎭᏂᏙᎸ, ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴ ᎬᏩᏍᏓᏩᏗᏙᎯ, ᎾᏍᏓᏯ ᏧᎬᏩᎶᏗ ᎤᏂᎯ ᎤᏁᎳᎲᎯ ᎤᏤᎵᎪᎯ ᏭᏂᏴᏍᏗᏱ.
Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
24 ᎬᏩᏍᏓᏩᏗᏙᎯᏃ ᎬᏩᏍᏆᏂᎪᏎᎴ ᎾᏍᎩ ᏄᏪᏒᎢ. ᎠᏎᏃ ᏥᏌ ᏔᎵᏁ ᎢᎤᏁᏨ, ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᏗᏥᏲᎵ. ᎾᏍᏓᏯ ᎾᏍᎩ ᎨᏅᎢᏍᏗ ᎨᏒ ᎠᎾᎵᏍᎦᏍᏙᏗᏍᎩ, ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏤᎵᎪᎯ ᏭᏂᏴᏍᏗᏱ.
Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
25 ᎤᏟ ᎠᎯᏗᏳ ᎨᎻᎵ ᏴᎩ ᎦᏌᏁᎾᏛᏗᏱ ᎤᎦᏛᎴᎯᏍᏗᏱ, ᎠᏃ ᎤᏪᎿᎭᎢ ᏴᏫ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏤᎵᎪᎯ ᏭᏴᏍᏗᏱ.
Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
26 ᎤᎶᏒᏍᏔᏅᎯᏃ ᎤᏂᏍᏆᏂᎪᏍᎨᎢ, ᎯᎠ ᏂᏓᎾᏓᏪᏎᎮᎢ, ᎦᎪᎨ ᏰᎵ ᎦᏰᏥᏍᏕᎸᏗ?
Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
27 ᏥᏌᏃ ᎾᏍᎩ ᏚᎧᎿᎭᏅ, ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎢ, ᏴᏫ ᎨᏒ ᎾᏍᎩ ᎢᎬᏛᏁᏗ ᏂᎨᏒᎾ, ᎤᏁᎳᏅᎯᏍᎩᏂ ᎨᏒ ᎥᏝ; ᎤᏁᎳᏅᎯᏰᏃ ᎨᏒ ᏂᎦᎥ ᎪᎱᏍᏗ ᎢᎬᏛᏁᏗ.
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
28 ᎿᎭᏉᏃ ᏈᏓ ᎤᎴᏅᎮ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᎬᏂᏳᏉ ᎠᏴ ᏂᎦᏗᏳ ᎣᎬᏕᏦᏅ, ᎠᎴ ᏂᎯ ᎢᏨᏍᏓᏩᏕᏅ.
Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
29 ᏥᏌᏃ ᎤᏁᏨ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎢ; ᎤᏙᎯᏳᎯᏯ ᎯᎠ ᏂᏨᏪᏎᎭ, ᎥᏝ ᎩᎶ ᏰᎭ ᎾᏍᎩ ᎤᏮᏕᏨᎯ ᎢᎨᏎᏍᏗ ᎠᏓᏁᎸᎢ, ᎠᎴ ᎠᎾᎵᏅᏟ, ᎠᎴ ᏧᏙ, ᎠᎴ ᎤᏙᏓ, ᎠᎴ ᎤᏥ, ᎠᎴ ᎤᏓᎵᎢ, ᎠᎴ ᏧᏪᏥ, ᎠᎴ ᏚᎶᎨᏒᎢ, ᎠᏴ ᎨᏒ ᏅᏗᎦᎵᏍᏙᏗᏍᎨᏍᏗ, ᎠᎴ ᎣᏍᏛ ᎧᏃᎮᏛ ᏅᏗᎦᎵᏍᏙᏗᏍᎨᏍᏗ,
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
30 ᎾᏍᎩ ᎪᎯ ᎨᏒ ᎠᏥᏁᏗ ᏂᎨᏒᎾ ᎨᏒ ᎠᏍᎪᎯᏧᏈ ᎢᏳᏩᎫᏗ ᎤᎶᏒᏍᏗ ᏓᏓᏁᎸᎢ, ᎠᎴ ᎠᎾᎵᏅᏟ, ᎠᎴ ᏧᏙ, ᎠᎴ ᏧᏥ, ᎠᎴ ᏧᏪᏥ, ᎠᎴ ᏕᎦᎶᎨᏒᎢ, ᎠᎩᎵᏲᎢᏍᏗ ᎨᏒ ᏔᎵ ᎤᏛᏗ; ᏐᎢᏱᏃ ᏗᎨᏒ ᎤᎵᏍᏆᏗᏍᏗ ᏂᎨᏒᎾ ᎬᏂᏛ. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 ᎠᏎᏃ ᎤᏂᏣᏔ ᎾᏍᎩ ᎢᎬᏱ ᏥᎩ, ᎣᏂ ᎨᏎᏍᏗ; ᎣᏂᏃ ᏥᎩ, ᎢᎬᏱ ᎨᏎᏍᏗ.
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
32 ᎦᏅᏅᏃ ᎠᎾᎢᏎ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᏣᏂᎦᏖᎢ; ᏥᏌᏃ ᎢᎬᏱ ᏚᏪᏅᎡᎴᎢ; ᎤᏂᏍᏆᏂᎪᏎᏃ; ᎾᏍᎩᏃ ᎠᎾᎵᏍᏓᏩᏗᏒ ᎠᏂᏍᎦᎢᎮᎢ. ᏔᎵᏁᏃ ᏚᏯᏅᎲ ᏔᎳᏚ ᎢᏯᏂᏛ, ᎤᎴᏅᎮ ᏚᏃᏁᎴ ᎾᏍᎩ ᎢᏳᎵᏍᏓᏁᎵᏓᏍᏗ ᎨᏒᎢ.
Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
33 [ ᎯᎠ ᏂᎦᏪᏍᎨᎢ; ] ᎬᏂᏳᏉ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᏫᏗᎦᏘ; ᎠᎴ ᏴᏫ ᎤᏪᏥ ᏙᏓᏰᏥᏲᏏ ᏄᏂᎬᏫᏳᏒ ᎠᏥᎸ ᎠᏁᎶᎯ ᎠᎴ ᏗᏃᏪᎵᏍᎩ ᏙᏓᎨᏥᏲᎯᏎᎵ; ᎠᎴ ᏙᏓᎬᏭᎪᏓᏁᎵ ᎤᏲᎱᎯᏍᏗᏱ, ᎠᎴ ᏧᎾᏓᎴᏅᏛ ᏴᏫ ᏫᏙᏛᏂᏲᎯᏎᎵ;
Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
34 ᎠᎴ ᏓᎬᏩᏐᏢᎢᏍᏔᏂ, ᎠᎴ ᏓᎬᏩᎵᎥᏂᎵ, ᎠᎴ ᏙᏓᎬᏩᎵᏥᏍᏈ, ᎠᎴ ᏓᎬᏩᎵ; ᏦᎢᏁᏃ ᎢᎦ ᏔᎵᏁ ᏙᏛᎠᎴᏂ.
waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
35 ᏥᎻᏃ ᎠᎴ ᏣᏂ, ᏤᏈᏗ ᏧᏪᏥ ᎬᏩᎷᏤᎴᎢ, ᎯᎠ ᏄᏂᏪᏎᎢ, ᏔᏕᏲᎲᏍᎩ, ᏍᎩᎾᏚᎵᎭ ᎢᏍᎩᎾᏛᏁᏗᏱ ᏄᏍᏛ ᎢᏍᏛᏔᏲᏎᏗ ᎨᏒᎢ.
Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
36 ᎯᎠᏃ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᎦᏙᏃ ᎢᏍᏓᏚᎵ ᎢᏍᏛᏯᏛᏁᏗᏱ?
Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
37 ᎯᎠᏃ ᏂᎬᏩᏪᏎᎴᎢ, ᏍᎩᎾᎵᏍᎪᎸᏓᏏ, ᎾᏍᎩ ᏦᎩᏂᏗᏱ, ᎠᏏᏴᏫ ᎯᎦᏘᏏᏗᏢ, ᏐᎢᏃ ᎯᎦᏍᎦᏂᏗᏢ, ᏣᏤᎵ ᎦᎸᏉᏗᏳ ᎨᏒᎢ.
Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
38 ᎠᏎᏃ ᏥᏌ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᎥᏝ ᏱᏍᏗᎦᏔᎭ ᏄᏍᏛ ᎢᏍᏗᏔᏲᎯᎲᎢ. ᏥᏌ ᏰᎵᏉ ᎨᏍᏓᏗᏔᏍᏗ ᎤᎵᏍᏈᏗ ᎾᏍᎩ ᎠᏆᏗᏔᏍᏗ ᏥᎩ? ᎠᎴ ᏗᎦᏰᏍᏓᏬᏍᏗ ᎾᏍᎩ ᏗᏓᏬᏍᏗ ᎨᏒ ᎾᏍᎩ ᎥᏆᏬᏍᏙᏗ ᏥᎩ?
Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
39 ᎯᎠᏃ ᏂᎬᏩᏪᏎᎴᎢ, ᏰᎵᏉ. ᏥᏌᏃ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ, ᎤᏙᎯᏳᎯ ᏓᏍᏓᏗᏔᎯ ᎤᎵᏍᏈᏗ ᎾᏍᎩ ᎠᏴ ᎠᏆᏗᏔᏍᏗ ᏥᎩ, ᎠᎴ ᏗᏓᏬᏍᏗ ᎨᏒ ᎠᏴ ᎥᏆᏬᏍᏙᏗ ᏥᎩ, ᎾᏍᎩ ᏙᏓᏰᏍᏓᏬᏍᏔᏂ;
Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
40 ᎤᏪᏗᏱᏍᎩᏂ ᎠᏉᎸ ᏥᎦᏘᏏ ᎢᏗᏢ, ᎠᎴ ᏥᎦᏍᎦᏂ ᎢᏗᏢ, ᎥᏝ ᎠᏴ ᎠᏆᏓᏁᏗ ᏱᎩ; ᎤᏅᏒᏍᎩᏂ ᎾᏍᎩ ᎨᎦᏛᏅᎢᏍᏓᏁᎸᎯ ᏥᎩ
amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
41 ᎠᏍᎪᎯᏃ ᎢᏯᏂᏛ ᎤᎾᏛᎦᏅ, ᎤᎾᎴᏅᎮ ᎤᏣᏘ ᎡᏍᎦ ᏚᏂᏰᎸᎾᏁᎴ ᏥᎻ ᎠᎴ ᏣᏂ.
Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
42 ᎠᏎᏃ ᏥᏌ ᏫᏚᏯᏅᎲ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ; ᎢᏥᎦᏔᎭ ᎾᏍᎩ ᎤᏂᎬᏫᏳᎯ ᎨᏥᏰᎸᎢ ᎨᏒ ᏧᎾᏓᎴᏅᏛ ᏴᏫ ᏓᏁᏩᏗᏒᎢ, ᏗᎬᏩᎾᏁᎶᏙᏗᏱ ᎾᏅᏁᎰᎢ; ᏧᏂᎸᏉᏗᏃ ᎨᏒ ᎬᏩᎾᏓᎵᏁᎯᏕᎰᎢ.
Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
43 ᏂᎯᏍᎩᏂ ᎢᏤᎲ ᎥᏞᏍᏗ ᎾᏍᎩ ᏱᏂᏨᏁᏍᏗ; ᎩᎶᏍᎩᏂ ᎠᏥᎸᏉᏗ ᎢᏳᎵᏍᏙᏗᏱ ᎤᏚᎵᏍᎨᏍᏗ, ᎾᏍᎩ ᎡᏥᏅᏏᏓᏍᏗ ᎨᏎᏍᏗ.
Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
44 ᎠᎴ ᎩᎶ ᏂᎯ ᏂᏣᏛᏅ ᏄᎬᏫᏳᏒ ᎢᏳᎵᏍᏙᏗᏱ ᎤᏚᎵᏍᎨᏍᏗ, ᎾᏍᎩ ᏂᎦᏛ ᎬᏩᏅᏏᏙᎯ ᎨᏎᏍᏗ.
Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
45 ᎾᏍᏉᏰᏃ ᏴᏫ ᎤᏪᏥ ᎥᏝ ᏳᎷᏨ ᎪᎱᏍᏗ ᎠᎦᏛᏁᏗᏱ, ᎪᎱᏍᏗᏍᎩᏂ ᎤᏓᏛᏁᏗᏱ, ᎠᎴ ᎬᏅ ᏧᏲᎯᏍᏗᏱ ᏧᎫᏴᏙᏗᏱ ᎤᏂᏣᏘ.
Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
46 ᏤᎵᎪᏃ ᎤᏂᎷᏤᎢ, ᎠᎴ ᎾᏍᎩ ᏤᎵᎪ ᎢᎤᏄᎪᏨ ᎠᎴ ᎾᏍᎩ ᎬᏩᏍᏓᏩᏗᏙᎯ, ᎠᎴ ᎤᏂᏣᏘ ᏴᏫ, ᏗᎨᏫ ᏆᏗᎻᏯ, ᎾᏍᎩ ᏗᎻᏯ ᎤᏪᏥ, ᎤᏬᎴ ᏅᏃᎱᎶᏗ ᎠᏚᎳᏗᏍᎨᎢ.
Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
47 ᎤᏛᎦᏅᏃ ᎾᏍᎩ ᏥᏌ ᎾᏎᎵᏗ ᎡᎯ ᎨᏒᎢ, ᎤᎴᏅᎮ ᎤᏪᎷᏁ, ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎢ, ᏕᏫ ᎤᏪᏥ, ᏥᏌ, ᏍᎩᏙᎵᎩ.
Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
48 ᎤᏂᏣᏖᏃ ᎬᏩᎬᏍᎪᎸᏁ ᎬᏩᏁᏤᎴ ᎡᎳᏪᏱ ᎤᏮᏗᏱ; ᎠᏎᏃ ᎤᏟᏉ ᎢᎦᎢ ᎤᏪᎷᏁᎢ, ᏕᏫ ᎤᏪᏥ ᏍᎩᏙᎵᎩ, ᎠᏗᏍᎨᎢ.
Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
49 ᏥᏌᏃ ᎤᎴᏫᏍᏔᏅ ᎤᏁᏤ ᏩᏥᏯᏅᏗᏱ. ᎤᏂᏯᏅᎮᏃ ᏗᎨᏫ, ᎯᎠ ᏄᏂᏪᏎᎴᎢ, ᎤᎦᎵᏍᏗᏉ ᎭᏓᏅᏓᏓ; ᏔᎴᎲᎦ; ᏗᏣᏯᏂᎭ.
Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
50 ᎾᏍᎩᏃ ᎤᏓᎢᏅ ᎤᏄᏬ ᏚᎴᏁᎢ, ᎠᎴ ᏥᏌ ᏭᎷᏤᎴᎢ.
Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
51 ᏥᏌᏃ ᎤᏁᏨ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᎦᏙ ᏣᏚᎵ ᎬᏯᏛᏁᏗᏱ? ᏗᎨᏫᏃ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᏣᎬᏫᏳᎯ, ᎥᎠᎩᎪᏩᏛᏗᏱ [ ᎠᏆᏚᎵᎭ.]
Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
52 ᏥᏌᏃ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ, ᎮᎾᏉᏃ; ᏦᎯᏳᏒ ᏣᏍᏕᎸ. ᎩᎳᏉᏃ ᎢᏴᏛ ᎬᏩᎪᏩᏛᏗ ᏄᎵᏍᏔᏁᎢ, ᎠᎴ ᎤᏍᏓᏩᏛᏎ ᏥᏌ ᎠᎢᏒᎢ.
Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.

< ᎣᏍᏛ ᎧᏃᎮᏛ ᎹᎦ ᎤᏬᏪᎳᏅᎯ 10 >