< Y Checho Y Apostoles Sija 26 >

1 AYONAE si Agripa ilegña as Pablo: Jupetmite jao na uncuentos pot jago namaesa. Ayonae si Pablo jaestira mona y canaeña ya manope pot güiya namaesa.
Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Za ka iya kare kan ka.” Sai Bulus ya daga hannunsa ya fara kare kansa.
2 Magofyo ray, Agripa, sa jufanope pot guajo gui menamo pago na jaane, pot todo y mafaaelajo ni y Judio sija.
“Ina farinciki, ya sarki Agaribas, game da saran da Yahudawa ke kawowa a kaina yau;
3 Yan pot y jutungo na jago untungo todo y costumbre yan y finaesen gui entre y Judios; pot enaomina jutayuyut jao na con pasensiamo umaecungogyo.
musamman ma don kai masani ne game da al'adun Yahudawa da al'amuransu. Don haka, ina rokanka ka yi hakuri ka saurare ni.
4 Y jaanejo desde y pinatgonjo, ni y finenana gui entre y nasionjo yan guiya Jerusalem, todo y Judios tumungo.
Hakika, dukan Yahudawa sun san yadda na yi rayuwa ta daga kurciyata a kasa ta, da kuma Urushalima.
5 Matungojayo desde y tutujonña, yaguin manmalago masangan, na taemanoja y mas tunas na secta y religionta, jumajanaoyo taegüije y Fariseo.
Sun san ni tun farko, kuma yakamata su yarda cewa na yi rayuwa kamar Bafarase, darikan nan mai tsatsauran ra'ayi ta addininmu.
6 Ya pago, tumotojgueyo ya majus gayo pot y ninanggan y promesa ni y jafatinas si Yuus gui mañaenata.
Yanzu ina tsaye a nan dominn a shari'anta ni, saboda alkawalin da Allah ya yi wa ubanninmu.
7 Ni y manmaprometa y dose tribus, masestbeja si Yuus jaane yan puenge, mananangga na ufato. Ya pot ayo na ninangga ray Agripa, na mafaaelayo ni y Judio sija.
Domin wannan shine alkawalin da kabilunmu goma sha biyu suka sa zuciya su karba, yayin da suke yin sujada da himma ga Allah dare da rana. Saboda wanan bege, Sarki Agaribas, Yahudawa ke tuhuma ta.
8 Jaftaemano majusga y tijongguiyon entre jamyo, na si Yuus janacajulo y manmatae?
Me ya sa wani zai yi tunani cewa abin mamaki ne Allah ya ta da mattatu?
9 Guajo magajet na jujaso gui jinalomjo, na nesesitayo jufatinas megae contra y naan Jesus Nasareno.
Da, na yi tunanin yin abubuwa gaba da sunan Yesu Banazarat.
10 Ya jufatinas este locue guiya Jerusalem; ya megae na mañantos jupreso, anae manresibeyo ninasiña guinin y magas mamale; ya anae para ufanmapuno, junae vosso contra sija.
Na yi wadanan a Urshalima. Na kulle masu bi da yawa a kurkuku, sanadiyar iko da na samu daga wurin manyan firistoci, kuma da ake kashe su ma, ina ba da goyon baya.
11 Ya jucastiga sija gui sinagoga, ya juprocura na junafanman chatfino contra si Yuus; ya pot gogoslalaloyo contra sija, jupetsigue sija achogja asta otro siuda sija.
Na wahalshe su sau dayawa a cikin dukan majamiu ina kuma yin kokari in tilasta masu su yi sabo. Na yi gaba mai zafi da su kuma na tsananta masu har zuwa birane na wadansu kasashe.
12 Ya anae jumajanaoyo para Damasco yan y ninasiña guinin y magas mamale sija,
A sa'anda nake yin wannan, na tafi Dimashku da izinin manyan firistoci;
13 Y taloane, O ray, julie gui chalan y candet guinin y langet, na malagña qui y ininan y atdao, ya manina gui oriyajo yan ayo y mangachochongjo manjanao.
a cikin tafiyata kuma, da tsakar rana, ya sarki, na ga haske daga sama da ya fi rana sheki, ya haskaka kewaye da ni da kuma wadanda ke tafiya tare da ni.
14 Ya anae mamodongjam todo gui jilo oda, jujungog y inagang na jacuentuseyo gui fino Hebreo, ilegña: Saulo, Saulo, jafa na unpetsisigueyo? mapot para jago y unfamateg contra y títuca.
Da dukanmu muka fadi kasa, na ji wata murya na magana da ni a harshen Ibraniyawa tana cewa, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani? Yana da wuya ka hauri abin da ke mai tsini.'
15 Ya ilegco: Jaye jao Señot? ya ilegña: Guajo si Jesus ni y unpetsisigue.
Sai na ce, 'Wanene kai ya Ubangiji?' Ubangiji ya amsa, 'Ni ne Yesu wanda kake tsanantawa.
16 Lao, cajulo ya untojgue; sa jufatoigüe jao pot este na jinaso, para junaministro jao yan untestigo ni este sija na güinaja y liniimo, yan ayo sija y pot y jufatoigüe jao;
Yanzu ka tashi tsaye domin saboda wannan dalili ne na bayyana gare ka in sanya ka, ka zama bawa da mashaidi na game da abubuwan da ka sani a kaina yanzu da wadanda zan bayyana maka daga bisani;
17 Junalibre jao gui pueblo yan y Gentiles, ya pago junajanao jao para iya sija,
Zan kubutar da kai daga wurin mutane da kuma al'ummai da zan aike ka wurinsu,
18 Para unbaba y atadogñija, yan unbira sija gui jemjom para y manana, yan y ninasiñan Satanas para as Yuus, ya ujaresibe y inasiin y isaoñija, yan erensia gui entalo ayo sija y manafangasgas pot y jinenggue ni y gaegue guiya guajo.
domin ka bude idanunsu ka juyo su daga duhu zuwa haske da daga ikon Shaidan zuwa ga Allah, domin su karbi gafarar zunubai da gado da zan ba wadanda na kebe wa kaina ta wurin bangaskiya gare ni.'
19 Ya pot ayo, ti chatmatagoyo, O ray Agripa, para y vision y langet:
Saboda haka, sarki Agaribas, ban yi rashin biyayya da wahayin da na gani daga sama ba;
20 Lao jusangane finenana ayo sija y mangaegue Damasco, yan iya Jerusalem, yan todo y tano Judea, yan y Gentiles, na ufanmañotsot ya ujabira sija para as Yuus, yan ufanmachocho y chechoñija ni y para mañotsot.
amma, da farko ga wadanda ke a Dimashku, sa'annan a Urushalima da kasar Yahudiya gaba daya, da dukan Al'ummai, na yi wa'azi domin su tuba su kuma juyo ga Allah, su yi ayyukan da suka chanchanci tuba.
21 Sa pot este sija na maconeyo ni y Judios gui guimayuus para jumapuno.
Domin wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a cikin haikali kuma suke kokari su kashe ni.
22 Lao jatacayo y inayudan Yuus, ya jusisigueja asta pago na jaane, mannanaeyo testimonio parejoja y diquique yan y dangculo; taya jusasangan na ayo y ufato ni y sinangan Moises yan y proteta sija;
Allah ya taimake ni har wa yau, domin in iya tsayawa gaban mutane kanana da manya, in bada shaida game da iyakar abin da annabawa da Musa suka fada zai faru;
23 Na si Cristo, nesesitagüe ufamadese, ya güiya ufinenana, pot ucajulo guinin y manmatae, ufannae candet gui pueblo yan y Gentiles.
wato lallai Almasihu zai sha wahala, ya kuma zama na farko da za'a rayar daga matattu ya kuma yi shelar haske zuwa ga mutanen Yahudawa da Al'ummai.”
24 Ya anae cumuecuentos, umagang si Festo ni y dangculo na inagangña, ilegña: Caduco jao Pablo: megae na tiningo ninacaduco jao.
Da Bulus ya gama kare kansa, Festas ya yi magana da babban murya, “Bulus, kana hauka; yawan iliminka yasa ka hauka.”
25 Lao si Pablo ilegña: Ti caducoyo Festo; lao jusasangan y sinangan ni y magajet yan y tinas.
Amma Bulus ya ce, “Ba na hauka, ya mai girma Festas; amma da karfin zuciya nake fadi kalmomin gaskiya da na natsuwa.
26 Sa y ray jatungoja estesija, cumuentosyoja gui menaña locue libre; sa seguroyo na taya güine sija na güinaja umanaatog guiya güiya; sa estesija, ti manmafatinas gui rincon.
Saboda sarkin ya san wadannan abubuwa duka; shi ya sa nake magana gabagadi, don na hakikance cewa, ba abin da ke a boye gare shi; gama ba a yi wadannan abubuwa a boye ba.
27 Ray Agripa, unjonggue y profeta sija? jutungo na unjonggue.
Ko ka gaskanta da annabawa, Sarki Agaribas? Na sani ka gaskanta.”
28 Ayonae si Agripa ilegña as Pablo, Canaja unnamamañañayo para juquilisyano.
Agaribas ya ce wa Bulus, “A cikin karamin lokaci kana so ka rinjaye ni ka mai da ni Krista?”
29 Ya si Pablo ilegña. Malagoyo as Yuus, na ti jagoja, lao todo ayo sija y jumungogyo pago na jaane, ufantaegüine iya guajo, fuera di y mapresujo.
Bulus ya ce, “Ina roko ga Allah, domin ko a karamin lokaci ko a dogon lokaci, ba kai kadai ba, amma har da wadanda ke sauraro na yau su zama kamar ni, amma ban da wadannan sarkokin.”
30 Ya anae munjayan jasangan este, cumajulo y ray yan y magalaje, yan Bernise, yan ayo sija y mangachongñiñija manmatachong.
Sai sarki ya tashi tsaye tare da gwamna da Barniki da dukan wadanda ke zaune tare da su;
31 Ya anae mañuja, manguentos uno yan y otro, ilegñija: Taya finatinasña este na taotao, na jamerese y finatae, pat umapreso.
da suka bar dakin taron, suka ci gaba da magana da juna suna cewa, “Wannan mutum bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ko kuma dauri ba.”
32 Ayonae ilegña si Agripa as Festo: Este na taotao, umanalibre, yaguin ti jagagao jinisgaña gui as Sesat.
Agaribas ya ce wa Fastos, “Da mutumin nan bai daukaka kara zuwa ga Kaisar ba da an sake shi.”

< Y Checho Y Apostoles Sija 26 >