< Lucas 23 >

1 Y se ardiñó sari ocola sueti, y lo lligueráron á Pilato.
Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
2 Y se chitáron á acusarle, penando: A ocona terelamos alachado pervirtiendo á amari sueti, y vedando platisarar jayere á Cæsar, y penando que ó sinela Christo Crallis.
Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
3 Y Pilato le puchabó, y penó: ¿Sinelas tucue o Crallis es Chuti? Y ó le rudeló penando: Tucue lo penelas.
Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
4 Penó Pilato á os Manclayes es Erajais, y á la sueti: Chichi, sos sinela choro alachelo andré ocona manu.
Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
5 Tami junos insistian, penando: Terela alborotado a sueti sat la beda, sos chibela por sari la Judéa, comenzando desde o chim de Galiléa, disde acoi.
Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
6 Pilato, sos juneló penar Galiléa, puchabó si sinaba de Galiléa.
Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
7 Y pur chaneló, que sinaba e jurisdicion de Herodes, lo bichabó á Herodes: sos al chiros socababa tambien andré Jerusalém.
Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
8 Y Herodes pur dicó á Jesus, se alendó baribu. Presas de baribu chiros le terelaba camelado dicar, presas habia junelado penar de ó barias buchias, y fronsaperaba dicarle querelar alguno zibo.
Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
9 Le quereló pues baribustrias preguntas: Tami ó le rudelaba chichi.
Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
10 Y sinaban os Manclayes es erajais, y os Libanes acusandole silamente.
Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
11 Y Herodes sat desqueres jundunáres ó despreció: y caquerandole le quereló chitar yeque conel parno, y aver begai o limbidió á Pilato.
Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
12 Y ocola chibes se quereláron monres Herodes y Pilato; presas palal sinaban daschmanuces entre sí.
A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
13 Pilato pues araqueró á os Manclayes es erajais, y á os Barandéres, y á la sueti.
Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
14 Y les penó: Terelais lanelado á mangue ocona manu, sasta pervertidor e sueti; y diquelad que puchabándole menda anglal de sangue, na alaché andré ocona manu yeque de ocolas buchias chorias de que o acusais.
ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
15 Ni Herodes Crallis: presas sangue bichabé á ó, y he acoi que se ha probisarado chichi, sos merezca meripen.
Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
16 Y andiar le despandaré despues de terelar curado.
Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
17 Y debisaraba despandarles yeque estardo andré o chibes e fiesta.
18 Y sari a sueti diñó goles catanés, penando: Querelad merar a ocona, y despandanos á Barrabás.
Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
19 Ocona habia sinado bucharado andré l’estaripel por yeque sedicion ardiñada andré o foros, y por yeque mordipen.
(Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
20 Y Pilato les chamulió de nuevo, camelando despandar á Jesus.
Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
21 Tami junos limbidiaban á diñar goles, penando: A la trijul con ó, A la trijul con ó.
Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
22 Y ó a trincha begai les penó: ¿Pues qué choro ha querdi ocona? Menda na alachelo andré ó necautia causa de meripen: le curelaré pues y le despandaré.
Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
23 Tami junos insistian mangando á goles bares, que sinase trijulado, y ardiñaban butér sus goles.
Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
24 Y Pilato penchabó, que se querelara ma junos mangaban.
Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
25 Y les despandó á ó sos por sedicion, y mordipen habia sinado bucharado andré l’estaripel, al sos habian mangado: y entregisaró á Jesus á las bastes de junos.
Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
26 Y pur lo lligueráron, ustiláron yeque manu de Cyrene, sos se hetó Simón, sos abillaba de yeque cosque: y le carguisaráron la trijul, somia que la lliguerase palal de Jesus.
Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
27 Y le plastañaban yeque plastañi bari de sueti, y de cadchias, sos le plañian y orobaban.
Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
28 Tami Jesus? límbidiandose hacia siras, les penó: Dugidas de Jerusalém, na orobeis opré mangue; antes orobad opré jirias matejas, ta opré jires chaborés.
Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
29 Presas abillarán chibeses andré que penarán: Majaradas as estériles, y as porias, sos na concibiéron, y as chuchai sos na diñáron de mamisarar.
Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
30 Entonces se chibarán á penar á as playas: Perad opré amangue: y á os bures: Ucharadnos.
Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
31 Presas si andré carschta bardry querelan ocono, ¿andré a seca, que se querelará?
Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
32 Y lligueraban tambien sat ó dui averes, sos sinaban chores, somia mulabarlos.
Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
33 Y pur bigoreáron á o stano, sos se heta de la Calavéra, le trijuláron oté; y os dui randés, yeque á la bastari, y aver á la can.
Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
34 Tami Jesus penaba: Dada, ojabesalos: presas na chanelan, ma querelan. Y dividiendo desqueres talalorés, bucháron sustirias.
Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
35 Y a sueti sinaba dicando, y os Manclayes catanamente sat junos o denostabelaban, y penaban: A averes chibó lacho, listrabese á sí matejo, si ocona sinela o Christo, o camelado de Debél.
Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
36 Le caqueraban tambien os jundunares, chalando sunparal á ó, y chitandole anglal vinagre.
Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
37 Y penando: Si tucue sinelas o Crallis es Chuti, listrabelate á tun matejo.
Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
38 Y sinaba opré ó yeque titulo libanado andré letras Griegas, Latinas y Ybuchias: Ocona sinela o Crallis es Chuti.
Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
39 Y yeque de ocolas randes, sos sinaban luanados, o injuriaba, penando: Si tucue sinelas o Christo, listrabela á tun matejo, y á amangue.
Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
40 Tami o aver rudelando, le chingaró, penando: Ni aun tucue canguelas á Debél, sinando andré a mateja corypény?
Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
41 Aromali amangue urgiyamos por amaro grecos, presas ustilamos ma merecen amarias obras: tami ocona chichi choro ha querdi.
Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
42 Y penába á Jesus: Erañó, enjallate de mangue pur abillares á tun chim.
Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
43 Y Jesus le penó; Aromali te penelo, que achibes sinarás con-a-mangue andré o Paraiso.
Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
44 Y sinaba ya casi a ocana zobia, y sari a chiquen se ucharó de tinieblas disde a ocana nubia.
Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
45 Y se chitó oruné o Cam: y o velo e cangri se asparabó pré medio.
domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
46 Y Jesus diñando yeque gole baro, penó: Dada: andré tirias bastes encomiendo minrio ylo: y penando ocono, espiró.
Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
47 Y pur dicó o Centurion ma habia anacado, diñó chimusolano á Debél, penando: Aromali, ocona manu sinaba lacho.
Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
48 Y sari a sueti sos sunparal sinaba, pur dicaba ma anacaba, se limbidiaba curandose andré os chepés.
Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
49 Y sares os pincherados de Jesus, y as cadchias sos le habian plastañado de Galiléa, sinaban dicando oconas buchias de dur.
Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
50 Y he acoi yeque gacho araquerado Joseph, sos sinaba Barander, gacho lachó ta justo:
Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
51 Sos na habia consentido andré o consejo, ni andré os hechos de junos, de Arimathéa, foros e Judéa, sos ujaraba o chim de Debél.
shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
52 Ocona bigoreó á Pilato, y le mangó o trupos de Jesus.
Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
53 Y habiendole nicabado, lo involvisaró andré yeque sabana parni, y lo childó andré yeque sepulchro querdi andré un bur, anduque cayque disde entonces habia sinado childado.
Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
54 Y sinaba o chibes de Parasceve, y sunparal sinaba a Canché.
An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
55 Y abillando tambien as cadchias sos habian plastañado á Jesus desde Galiléa, dicáron o sepulchro, y a beda en que sinaba childado desquero trupos.
Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
56 Y limbidiandose, quináron bus ta unguentes; y reposáron a Canché sasta mandisarela a Eschastra.
Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.

< Lucas 23 >