< Lucas 10 >

1 Y despues de ocono araqueró o Erañó tambien averes setenta y dui; y os bichabó de dui en dui anglal de ó á saro foros y gau, aduque ó terelaba de abillar.
Bayan wadannan abubuwa, Ubangiji ya sake nada wadansu saba'in ya aike su biyu biyu, domin su tafi kowanne birni da wurin da yake niyyan zuwa.
2 Y les penaba! Aromali a mies sinela baribustri, tami os randiñadores frimés. Manguelelad pues al Erañó e mies, que bichabele randiñadores á desqueri mies.
Ya ce da su, “Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan sun yi kadan. Saboda haka kuyi addu'a sosai ga Ubangijin girbin, domin ya aiko da ma'aikata cikin gonarsa.
3 Chalad: He acoi menda bichabelo sangue, sasta brajias en medio de lueyes.
Ku tafi, duba na aike ku kamar 'yan raguna cikin kyarkyetai.
4 Na lliguereleis quisóbu, ni manrañea, ni calcos, ni aspasareis á cayque por o drun.
Kada ku dauki jakan kudi, ko jakar matafiyi, ko takalma, kada ku gai da kowa a kan hanya.
5 André o saro quer que chalareis, brotobo penelad: paz sinele á ocona quer.
Dukan gidan da ku ka shiga, ku fara cewa, 'Bari salama ta kasance a wannan gida.'
6 Y si sinare oté chaboro de paz, se chibará opré ó jiré paz; y si nanai, se limbidiará á sangue.
Idan akwai mutum mai salama a gidan, salamar ku za ta kasance a kansa, amma idan babu, salamar ku za ta dawo wurinku.
7 Y socabelad andré o matejo quer, jamando y piyando ma junos terelen, presas o randiñador digno sinela de desquero jayere. Na naqueleis de quer andré quer.
Ku zauna a wannan gidan, ku ci ku sha abin da suka tanada maku. Gama ma'aikaci ya wajibci ladansa. Kada ku bi gida gida.
8 Y andré o saro foros andré coin chalareis, y sangue ustilaren, jamelad ma sangue childaren anglal.
Dukan birnin da ku ka shiga kuma sun karbe ku, ku ci abin da suka sa a gabanku.
9 Y chibelad mistos á os merdés, sos andré ó terelare, y penadles: Se ha abillado sunparál á sangue o chim de Debél.
Ku warkar da marasa lafiyar da ke wurin. Ku ce da su, 'Mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
10 Tami si andré o foros andré que chalareis, na ustilaren sangue, abillando por desqueres maasqueres, penelad:
Amma dukan birnin da ku ka shiga, idan ba su karbe ku ba, ku tafi cikin titunansu, ku ce,
11 Aun o pracos, sos se ha pegado á amangue de jiré foros, chibelamos contra sangue: Chanelad no obstante, que ha abillado sunparal o chim de Debél.
'Ko kurar birninku da ta like a kafafunmu, mun karkabe maku ita a matsayin shaida a kanku! Amma ku sani mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
12 Sangue penelo, que andré ocola chibes sinará fetér a baji de Sodoma que de ocola foros.
Na gaya maku, a ranar shari'a Saduma za ta fi wannan birni samun sauki.
13 ¡Ysna de tucue, Corozain! ¡Ysna de tucue Bethsaida! Que si andré Tyro, y andré Sydón se hubiéran querdi as buchias, sos se han querdi andré sangue, chiros há que bestelados andré conel de gono y andré jaquestaro, hubieran querdi penitencia.
Kaiton ki, Korasinu! Kaiton ki, Baitsaida! Ayyuka masu girma da aka yi a cikinku, da an yi su a cikin Taya da Sidon, da sun tuba tuntuni a zaune cikin toka da tufafin makoki.
14 Aromali para Tyro, y Sydón, sinará andré o juicio fetér baji, que para sangue.
Amma a ranar shari'a Taya da Sidon za su fi ku samun sauki.
15 Y tucue, Capharnaúm, ardiñado disde o Charos, disde o butrón sinarás chibado ostely. (Hadēs g86)
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani har zuwa sama za a daukaka ki? Babu, za a gangarar dake har zuwa hadas. (Hadēs g86)
16 O sos junela á sangue, junela á mangue. Y ó sos girela á mangue, girela á ocola, sos mangue bichabó.
Wanda ya saurare ku ya saurare ni, wanda ya ki ku, ya ki ni, kuma wanda ya ki ni, ya ki wanda ya aiko ni.”
17 Y limbidiáron os setenta y dui sat pesquital, penando: Erañó, aun os bengues se nos sujetan andré tiro nao.
Su saba'in din suka dawo da murna, suna cewa, “Ubangiji, har ma aljanu suna yi mana biyayya, a cikin sunanka.”
18 Y les penó: Dicaba á Satanas sasta yeque maluno, sos peraba del Charos.
Sai Yesu ya ce masu, “Na ga Shaidan yana fadowa daga sama kamar walkiya.
19 Diquelais: que sangue he diñado sila de pirar opré gulistrabas, y birberechas, y opré saro o ezor e daschmanu: y chichi sangue dañará.
Duba, na ba ku iko ku taka macizai da kunamai, da kuma kan dukan ikon magabci, kuma ba zai iya yin illa a gareku ba ko kadan.
20 Tami andré ocono na asaseleis sangue: que os bengues os sinelen sujetos, antes asaselaos de que jires naues sinelan randados andré o Charos.
Amma duk da haka kada ku yi murna a kan wannan kadai cewa ruhohi suna yi maku biyayya, amma ku yi murna domin an rubuta sunayenku a cikin sama.”
21 André ocola mateja ocana se asaseló andré o Peniche, y penó; Díñelo á tucue chimusolano, Dada Erañó e Tarpe y de la pu, presas ucharaste oconas buchias, á os Chandes y peruiques, y as has chibado en dut a os chinores. Andiar sinela, Dada: presas andiar ha sinado de tun pesquital.
Cikin wannan lokacin, ya yi farin ciki kwarai cikin Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Na ba ka girma, ya Uba, Ubangijin sama da kasa. Domin ka rufe wadannan abubuwa daga masu hikima da ganewa, ka bayyana su ga wadanda ba koyayyu ba ne, kamar kananan yara. I, Uba gama haka ne ya gamshe ka.”
22 Sarias as buchias a mangue sinelan diñadas de minrio Dada. Y cayque chanela, coin sinela o Chaboro, sino o Dada, ni coin sinela o Dada, sino o Chaboro, y ocola, á sos lo camelare penar o Chaboro.
Dukan abu, Ubana ya damka su gare ni, kuma babu wanda ya san Dan, sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Dan. Sai kuma wanda Dan ya yi niyyar ya bayyana Uban a gareshi.”
23 Y limbidiándose hacia os discipules, penó: Majares as aquias, sos diquelan ma sangue diquelais.
Ya juya wajen almajiran, ya ce da su a kadaice, “Masu albarka ne su wadanda suka ga abin da kuke gani.
24 Presas á sangue penelo, que baribustres Prophetas, y Crallises camelaron dicar ma sangue diquelais, y na lo dicáron; y junelar ma junelais, y na lo juneláron.
Na fada maku, annabawa da yawa, da sarakuna da yawa sun so da sun ga abubuwan da kuke gani, amma ba su gani ba. Kuma sun so da sun ji abubuwan da kuke ji, amma ba su ji su ba.”
25 Y se ardiñó yeque Chande de la Eschastra, y le penó somia pesquilarle: ¿Duquendio, que quereláre somia terelar chipen deltó? (aiōnios g166)
Sai ga wani malamin shari'ar Yahudawa, ya zo ya gwada shi da cewa, “Malam, me zan yi domin in gaji rai na har abada?” (aiōnios g166)
26 Y ó le penó: ¿André á Eschastra qué sinela randado? ¿sasta lirenas?
Sai Yesu ya ce masa, “Yaya kake karanta abin da aka rubuta cikin shari'a?”
27 O rudelando penó: Camelarás al Erañó tun Debél de saro tun carlochin, y de sari tun ochi, y de sari tun sila, y de sari tun chaneleria: y á tun proximo sasta á tun matejo.
Ya amsa ya ce,”Dole ne ka kaunaci Ubangiji Allah da dukan zuciyarka, da dukan ranka da dukan karfinka, da dukan lamirinka. Ka kuma kaunaci makwabcinka kamar kanka.”
28 Y le penó: Mistos has rudelado: Querelad ocono, y vivisarás.
Yesu ya ce ma sa, “Ka amsa daidai, idan ka yi haka za ka rayu.”
29 O camelandose justificar á desquero matejo, penó a Jesus: ¿Y coin sinela minrio proximo?
Amma, malamin ya na so ya 'yantar da kansa, sai ya ce da Yesu, “To, wanene makwabcina?”
30 Y Jesus ustilando a varda, penó: Elabel chalaba ostely de Jerusalém á Jerichó, y diñó andré bastes de yeques randes, sos le randáron; y despues de terelarle curado, le mequeláron pas-mulo, y se chapescáron.
Ya amsa ya ce, “Wani mutum yana tafiya daga Urushalima za shi Yariko. Sai ya fada hannun mafasa, suka tube shi, suka kwace dukan abin da ya ke da shi, suka yi masa duka, suka bar shi kamar matacce.
31 Anacó pues, que nacaba por o matejo drun yeque erajai: y pur o dicó, nacó de muy dur.
Ya zama sai ga wani firist ya na bin wannan hanya, da ya gan shi sai ya bi ta gefe daya ya wuce.
32 Y andiar matejo yeque Levita, bigoreando sunparal de ocola stano, y dicandole, nacó de dur.
Haka kuma sai ga wani Balawi, sa'adda ya zo wurin, ya gan shi sai ya bi ta wani gefe ya wuce shi.
33 Tami yeque Samaritano, sos chalaba desquero drun, se bigoreó sunparal de ó: y pur le dicó, se lo diñó canrea.
Amma wani Basamariye, ya na tafiya sa'adda ya zo wurin da mutumin yake, sa'adda ya ga mutumin sai tausayi ya kama shi.
34 Y bigoreandose, le pandó as merdes, chibelando andré siras ampio y mol: y chibandolo opré desquero gra, lo lligueró a yeque mesuna, y tereló cuidado de ó.
Ya zo inda mutumin yake, ya daure masa raunukan da aka ji masa, yana shafa masu mai da ruwan inabi. Ya dora shi a kan dabbarsa ya kawo shi wurin kwana, ya kula da shi
35 Y aver chibes sicobó dui calés, y os diñó al julai, y le penó: Garabelamanguele: y o saro sos gastisareles de butér, menda á tucue lo diñare pur limbidie.
Washegari ya kawo dinari biyu, ya ba mai wurin kwanan ya ce 'Ka kula da shi, idan ma ka kashe fiye da haka, idan na dawo zan biya ka.'
36 ¿Coin de ocolas trin penchabelas que sinaba o proximo de ocola, sos diñó andré bastes es randes?
A cikinsu ukun nan, wanene kake tsammani makwabcin wannan mutum da ya fada hannun 'yan fashi?”
37 Ocola, rudeló o Chandé, sos tereló canrea sat ó: Pues cha, le penó, y querela tucue o matejo.
Sai malamin ya ce, “Wannan da ya nuna masa jinkai” Sai Yesu yace masa, “Ka je kai ma ka yi haka.”
38 Y anacó, que sasta sinasen andré drun, chaló Jesus andré yeque gau: y yeque cadchi, sos se hetó Martha, lo ustiló andré o quer de siró.
Sa'adda suke tafiya, sai ya shiga cikin wani kauye, sai wata mata mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 Y ocona terelaba yeque plañi, araquerada Maria, sos bejelada á os pindres e Erañoró, junelaba su varda.
Tana da 'yar'uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a kafafun Ubangiji tana jin abin da yake fadi.
40 Tami Martha sinaba ocupada gajere andré as haciendas e quer: y siró se abilló y penó: ¿Erañó, na diqueles, sasta minri plañi, mangue ha mequelado colcori somia querelar? penle pues, que mangue ayude.
Amma ita Marta ta na ta kokari ta shirya abinci. Sai ta zo wurin Yesu ta ce, “Ubangiji, ba ka damu ba 'yar'uwata ta bar ni ina ta yin aiki ni kadai? Ka ce da ita ta taya ni.”
41 Y o Erañó le rudeló, y penó: Martha, Martha, baribu cuidadosa sinelas, y andré baribustrias buchias te trajatelas.
Amma Ubangiji ya amsa ya ce da ita, “Marta, Marta, kin damu a kan abubuwa da yawa,
42 Aromali jomte solamente yeque buchi. Maria ha ustilado a aricata fetér, sos na le sinará nicobelada.
amma abu daya ne ya zama dole. Maryamu ta zabi abu mafi kyau, wanda ba za a iya kwace mata ba.”

< Lucas 10 >