< Лука 5 >

1 А еднаж, когато народът Го притискаше да слуша Божието слово, Той стоеше при Генисаретското езеро.
Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
2 И видя две ладии, спрени край езерото; а рибарите бяха излезли от тях и изпираха мрежите си.
Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
3 И като влезе в една от ладиите, която беше Симонова, помоли го да я отдалечи малко от сушата; и седна та поучаваше народа от ладията.
Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
4 И като престана да говори, рече на Симона: Оттегли ладията към дълбокото и хвърлете мрежите за ловитба.
Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
5 А Симон в отговор рече: Учителю, цяла нощ се трудихме и нищо не уловихме; но по Твоята дума ще хвърля мрежите.
Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
6 И като сториха това, уловиха твърде много риба, така щото се прокъсваха мрежите им.
Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
7 И извикаха съдружниците си от другата ладия да им дойдат на помощ; и те дойдоха и напълниха и двете ладии, до толкова, щото щяха да потънат.
Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
8 А Симон Петър, като видя това, падна пред Исусовите колене и каза: Иди си от мене, Господи, защото съм грешен човек.
Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
9 Понеже той и всички, които бяха с него, се учудиха на ловитбата на рибите що уловиха,
Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
10 също и Яков и Иоан, синове на Заведея, които бяха Симонови съдружници. А Исус рече на Симона: Не бой се; отсега човеци ще ловиш.
Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
11 И когато извлякоха ладиите на сушата, оставиха всичко и отидоха след Него.
Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
12 И когато беше в един от градовете, ето, човек, който беше цял прокажен, като видя Исуса, падна на лицето си и Му се помоли, казвайки: Господи, ако искаш можеш да ме очистиш.
Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
13 А Той простря ръка и се допря до него, и рече: Искам: бъди очистен! И на часа проказата го остави.
Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
14 И Той му заръча, никому да не каже това: Но, за свидетелство на тях, иди, каза, и се покажи на свещеника, и принеси за очистването си, според както е заповядал Моисей.
Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
15 Но още повече се разнасяше вестта за Него; и големи множества се събираха да слушат и да се изцеляват от болестите си.
Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
16 А Той се оттегляше в пустините и се молеше.
Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
17 И през един от тия дни, когато Той поучаваше, там седяха фарисеи и законоучители, надошли от всяко село на Галилея, Юдея и Ерусалим; и сила от Господа бе с Него да изцелява.
Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
18 И ето мъже, които носеха на постелка един болен човек, който беше паралитик; и опитаха се да го внесат вътре и да го сложат пред Него.
A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Но понеже не намериха през где да го внесат вътре, поради народа, качиха се на покрива, и през керемидите го спуснаха с постелката насред пред Исуса.
Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
20 И Той, като видя вярата им рече: Човече, прощават ти се греховете.
Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
21 Тогава книжниците и фарисеите почнаха да се препират, казвайки: Кой е Тоя, Който богохулствува? Кой може да прощава грехове, освен един Бог?
Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
22 Но Исус, като видя разискванията им, каза им в отговор: Защо разисквате в сърцата си?
Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
23 Кое е по-лесно, да река: Прощават ти се греховете, или да река: Стани и ходи?
Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
24 Но за да познаете, че Човешкият Син има власт на земята да прощава грехове, (рече на паралитика): Казвам ти: Стани, дигни постелката си, и иди у дома си.
Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
25 И начаса той стана пред тях, дигна това, на което лежеше, и отиде у дома си, като славеше Бога.
Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
26 И те всички се учудиха и славеха Бога, и, изпълнени със страх, казваха: Днес видяхме пречудни неща.
Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
27 След това Исус като излезе, видя един бирник, на име Левий, седящ в бирничеството, и рече му: Върви след Мене.
Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
28 Той остави всичко, стана и тръгна след Него.
Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
29 А Левий Му направи голямо угощение в къщата си; и имаше голямо множество бирници и други, които седяха на трапезата с тях.
Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
30 А фарисеите и техните книжници роптаеха против учениците Му, казвайки: Защо ядете и пиете с бирниците и грешниците?
Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
31 Исус в отговор им рече: Здравите нямат нужда от лекар, а болните.
Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
32 Не съм дошъл да призова праведните, но грешните на покаяние.
Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 И те Му рекоха: Иоановите ученици често постят и правят молитви, така и фарисейските, а Твоите ядат и пият.
Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
34 Исус им рече: Можете ли да накарате сватбарите да постят докато е с тях младоженецът?
Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
35 Ще дойдат, обаче дни, когато младоженецът ще се отнеме от тях; тогава, през ония дни, ще постят.
Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
36 Каза им още и притча: Никой не отдира кръпка от нова дреха да я тури на вехта дреха; инак и новата дреха се съдира, и кръпката от новата не прилича на вехтата.
Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
37 И никой не налива ново вино в стари мехове; инак, новото вино ще пръсне меховете, и то само ще изтече, и меховете ще се изхабят.
Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
38 Но трябва да се налива ново вино в нови мехове.
Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
39 И никой, след като е пил старо вино, не иска ново, защото казва: Старото е по-добро.
Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”

< Лука 5 >