< Uruyan Yuhana 7 >

1 Na nani nkata nyene unan kadura Kutelle yisin nasari anas inyi, imin ufunu unas unnasari inyi bara na ufuunu nwa ko kidowo, nan nya inye ba, sa kurawa ba, sa kitene naca ba.
Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace.
2 Nyene umon unan kadura Kutelle awa dak unuzu kusari nnucin nwui, ulenge na adinin kulap Kutelle nlai, asu kuculu nin liwui kang, udu kiti nanan kaddura nanas allenge na iwa yinin nani ilanza uyi nin kurawa ukal.
Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce,
3 “Na iwa lanza, uyi nin kurawa, sa atca, se ita nani kulap nitin nacin Kutelle.”
“Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.”
4 Nlanza ngbardang nalenge na iwa ti nani alape, iwa duru amui akut likure nin nakure anas a nas, alenge na iwa ti nani alap unuzu vat tilpinpin nanit iseraila.
Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.
5 Unuzo likuran Yahuda iwati anit amui likure nin aba alap, Unuzo likuran Reuben iwati anit amui likure nin a alap, Unuzo likuran Gad iwati anit amu likure ana naba kulap.
Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin, daga kabilar Ruben mutum 12,000, daga kabilar Gad mutum 12,000,
6 Unuzo likuran Asher iwati anit amui likure nin na aba alap, Unuzo likuran Naptali iwati anit amui likure nin na ba alap, Unuzo likuran Mannasah iwati anit amui likure nin na ba alap.
daga kabilar Asher mutum 12,000, daga kabilar Naftali mutum 12,000, daga kabilar Manasse mutum 12,000,
7 Unuzo likuran Simeon iwati anit amui likure nin na aba alap, Unuzo likuran Levi iwati anit amui likure nin na ba nalap, Unuzo likuran Issakar iwati anit amui likure nin na ba alap,
daga kabilar Simeyon mutum 12,000, daga kabilar Lawi mutum 12,000, daga kabilar Issakar mutum 12,000,
8 Unuzo likuran Zabalun iwati anit amui likure nin ba alap, Unuzo likuran Yusufu iwati anit amui likure nin ba alap, Unuzo likuran Banyamin iwati anit amui likure nin ba aba alap.
daga kabilar Zebulun mutum 12,000, daga kabilar Yusuf mutum 12,000, daga kabilar Benyamin mutum 12,000.
9 Na isu ile vat, nyene ligo nanit wa duku gbardang na umong wasa abatiza ba-unuzu vat nmyine, akura, anit nan tilem-iyisina nbun kutet tiigo, nin nbun kuzara iwa shon atuluk aboo, imin tilang kutca ndabino nacara mine,
Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu.
10 iwadi nyicu nin liwui lidia: “Utucu un Kutelle bitari, ulenge na asosin kutet tigo nin udu kiti kuzara!”
Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa, “Ceto na Allahnmu ne, wanda yake zaune a bisan kursiyi, da kuma na Ɗan Ragon.”
11 Vat na nan kadura Kutelle wa kilin kutet tigo nin nakune a inawan tene inas nlai, ituna tumuzuno kutyin ita ti muro mine kutyin nbun kutet tigo isu Kutelle usujada,
Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada,
12 iworo, “Uso nani! Liru, ngongong, njinjin, uzazinu, uyiko a likara udu kiti Kutelle sa ligan! Uso nani!” (aiōn g165)
suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn g165)
13 Umong nan nya nakune tirini, ayaghari ale nshono imon iboo, tutun inuzu nweri?
Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”
14 Meng woroghe, “Cikilari, fe yru,” ame belli, “Alele inughere ulenge na ina nuzu nan nya nniyu udia. Inani nakusu alutuk mine lau ata aboo nin nmyi kuzara.
Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.” Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan.
15 Bara nanere idi nbun kutet tigo Kutelle, idin sughe usujada kiti nlira kiyitik nin liring. Ame ule na a na asosin kitene kutete aba bagilinu ugudu me kitene mine.
Saboda haka, “suna a gaban kursiyin Allah suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa; kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.
16 Na iba lanzu kukpong sa ukotu nayi tutun ba, na uwui ngwagai nwai ba ri nani ba, sa imomon njujuzu.
‘Ba za su sāke jin yunwa ba; ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba. Rana ba za tă buga su ba,’ ko kuma kowane irin zafin ƙuna.
17 Bara kuzare na adi nan nya kiyitik kutet tigowe aba so unan libiya mi ine, aba dofinu ninghinu udu kigawa nmyen nlai, ame Kutelle ba wesu nani vat nmizin niyizi mine.”
Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu; ‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’ ‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’”

< Uruyan Yuhana 7 >