< Uruyan Yuhana 11 >

1 Iwa niyi kugosin nafo uca fikoro nbatizu njangarang. Iworai, “Fita u bata kilari nlira Kutelle nin bagadi, nan na le na idin su nlira nan nye.
Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
2 Na uwa bata kudaru nwucu nlirue na kudi ndas kutyi nlire ba, bara ina ni Awurmi kuning. Ima patilu kipin kilauwe nan nya tipui akut anas nin tiba.
Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
3 Nma ni ashaida aba nighe likara nsun anabci nayiri limui nin na kat aba akut kutocin, ima shonu ajassi nimon.”
Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
4 Ashaida abe inughere aca nzaitun aba nin tipitilla tiba tongo na ti yissin nbuun nCikilare nan nya in yie.
Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
5 Asa umong nferu ama cuci nani, ula ma nizu nan nya tinun mine uli anan nivira mine. Ulenge na apizira a lanza umong ukul ima molu nlongo libo we.
Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
6 Ashaida alele di nin likara nworu i tursu kitene kana bara uwuru wa juu kubi kongo na isu uanabce. Idi nin nakara nworu ikpilya nmyen miso nmii inin kuru ilanza uyie ukul nin na luba kubi kongo na ita usu.
Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
7 Kubi kongo na ima se imala ushaida mine, ku gbergenu kongo na kuna nuzu nan nya kuu kucomcom kun sali ligang masu likun nan ghinu. Ama li likara mine a molu nani. (Abyssos g12)
To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos g12)
8 Abi mine ma nonnu libau nan nya kipin kidia (na adin dursuzu uSodom nin Masar) kika na iwa kotun Cikilari mine ku kuca.
Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
9 Nan nya nayiri atat nin kagissin among vat nanit, akura, lilem nin mein iba yenju abi mine, a na ima yinnu nani i cisso abi mine kisset ba.
Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
10 Alenge na i sossin in yie ima su liburi libo inin su ubuki, har ma iniza imon filizunu kiti nado mine bara anan liru nin nuu Kutelle naba alele nati anitt alenge na issosin in yie ineo kang.
Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
11 Ama kimal nayiri atat nin kagisin nfip nlai unuzu kiti Kutelle ma piru nani ima fitu i yissin nin na bunu mine. Fiu fidya ma kifi alenge na iyene nani.
Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
12 Ima lanzu liwui li karau unuzu kitene kani ma woru nani, “Fitan idak kika!” Inung ma nin ghanu kitene kani nan nya kuwut, anan nivira mine yita in yenjue.
Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
13 Nan nya ku birie kone uzullunu nin lirtizu kutyen ikop in likure ba disu. Uzinlinu kutin ba molu anit amui kuzo, ale na iba lau nin lai iba lanzu fiu, a anan ti nlai ye ma lanzu fiu ini Kutelle Ngongong kitene kane.
A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
14 Uneu nbe kata. Sun uca! Unui un tatte din cinu dadai.
Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
15 Gono kadura kin zore wulsuno kulantung me, tiwui ti karau su uliru nanya in yie, i woro, “Kipin tigo in yie nlawa kipin tigo nCikilari nin Kristi. Ama su tigo har saligang.” (aiōn g165)
Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
16 Akune akut aba nin nanas ale na iwa sossin natet tigo nbun Kutelle inozo kutien ni timuro mine, indi Kutelle usajada.
Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
17 I woro, “Ti difi nafi liburi libo, Cikilari Kutelle, unan tigo kitene vat, ule na adi, a na awa di, bara na una yiruu akara adia fe umini na cizin tigowe.
suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
18 Ti myin wa nana ayi, amma tinana nayi fe toni nda. Kubi nda isu anan kul uwusu kedegen, fe nin ni a anabawa fe ku uduk katwa mine, anit alau, nin na leng na ina lanza fiu lissa fe, umunu anan sali nakara nin na nan nakara. A kubi ndafi umolu alenge na idin molusu anan yie.”
Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
19 Uhaikali Kutelle kitene kani iwa pun ina ni wa yene usanduki likawali me iwa yene nanya nhaikale. Nkanang nmalizunu, tiwui nin tutuzu kiti nin lirtizi kutyen a udissu natantani gbardang.
Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.

< Uruyan Yuhana 11 >