< Filibiya 2 >

1 In ma yinnu nwo unizu likara nanya Kristi duku. Inma yinnu nwo usoo mang unuzun suume. Inma yinnu nwo ligo nin Ruhu duku. Inma yinnu nwo nkunekune mi cancom nin suun bunu duku.
Idan akwai wani abin karfafawa cikin Almasihu. Idan da wata ta'aziyya daga kaunarsa. Idan akwai zumunta a Ruhu. Idan da tatausan jinkai da tausayi.
2 Tan ayiabo nin kulo nin kpiluzu urum ulele, iyitta nin suu urume, inin yita nin munu ati nanya Ruhu, anin suu nsu nimon irume.
Ku cika farin cikina don ku zama da tunani irin haka, kuna da kauna daya, kuna tarayya cikin Ruhu daya, ku kasance da manufa iri daya.
3 Yenje iwasu imonimon bara usuu nati sa ukpilizu unanzang. Na nonkon atime iyenje among nafo ikatin minu.
Kada ku yi komai cikin sonkai ko girman kai. A maimakon haka cikin zuciya mai tawali'u kowa na duban wadansu fiye da kansa.
4 Yenje iwa kpiliza ubelle nimon ile na idi ninsuwe cas, ama kpilizang imon su namong wang.
Kada kowa ya dubi bukatun sa, amma yana lura da bukatun wadansu.
5 Kpilizang libau longo na lidi lin Kristi Yesu wang.
Ku yi tunani cikin hanya wadda ke cikin Almasihu Yesu.
6 Awa yitta nin kulap Kutelle, ama na awa yaun lissosin me nin Kutelle nafo imon ilenge na ame ma minu ba.
Wanda ya yi zama cikin siffar Allah, bai mai da daidaitarsa da Allah wani abin da zai rike ba.
7 Awa na wese litime nya liti. Ayauna kulap kucin. Anuzu nin kidowon nit usurne. Iwa seghe nin yenju nafo unit.
Maimakon haka, ya wofintar da kansa. Ya dauki siffar bawa. Ya bayyana cikin kamannin mutane. An same shi a bayyane kamar mutum.
8 Awa toltin litime aso una dortun liru udun kul, ukul un kitene kuca.
Ya kaskantar da kansa, ya yi biyayya har ga mutuwa, mutuwa ta gicciye.
9 Bara nani Kutelle uni wa ghantighe. Awa ninghe lissa ubun kolome lissa.
Saboda haka Allah ya ba shi mafificiyar daukaka. Ya ba shi suna wanda yafi kowanne suna.
10 Awa tinane bara nanya lissa Yesu vat nalung ma tumnu, alung nalenge na idi kitene kani nin kutiin a nanya kutiin.
Domin a cikin sunan Yesu kowace gwiwa za ta durkusa, gwiwoyin wadanda ke cikin sama da kuma duniya da kuma karkashin duniya.
11 Awa sunani tutung bara kolome lilem ma punu abellin Yesu Kristi Cikilareri, udun gongon Kutelle Ucif.
Kuma kowanne harshe zai furta cewa Yesu Almasihu Ubangiji ne, zuwa daukakar Allah Uba.
12 Bara nani, anan suuning, nafo na idin dortu kolome liri, na se meng duku ba, ama nene gbardang ka nin salininghe, sun katwa ntuccu mine nin fiu nin ketuzu kiti.
Domin wannan kaunatattuna, kamar yadda kullum kuke biyayya ba sai ina nan kadai ba. Balle yanzu da bananan, ku yi aikin cetonku da tsoro da far gaba.
13 Bara Kutelleri di katwa nanya mine vat nin yinnu a usu katwa bara nmang me.
Gama Allah ne yake aiki a cikinku ku yi nufi duka da aikata abin da zai gamshe shi.
14 Sun ko iyapin imon sa ugbondulu sa mayardang.
Ku yi kowanne abu ba tare da gunaguni da gardama ba.
15 Sun katwa nin nile imone inan so sa alapi nin nono kidegen Kutelle sa indinon. Sun katwa nin nile imone bara inan balta nafo nkanang nanya yii, kitik kuji ku kwarkwok nin dirun fiu Kutelle.
Domin ku zama marasa abin zargi kuma masu gaskiya, 'ya'yan Allah marasa aibi. Ku yi haka domin ku haskaka kamar haske a cikin wannan duniya, a tsakiyar karkatacciyar da gurbatacciyar tsara.
16 Minon gangan tigbulan nlai bara inan se imon ile na imati gongon lirin Kristi. Kubere nmanin yinnu na nnasu uccum sa katwa kahem ba.
Ku rike kalmar rai da karfi domin in sami dalilin daukaka Almasihu a ranarsa. Sa'annan zan san cewa ban yi tseren banza ba, ban kuma yi wahalar banza ba.
17 Ama ko igutuni nafo unakpu ulau nanyan ni liti nin katwa in yinnu sa uyenu mine, idin su ayiabo, nkuru nsu ayiabo nanghinu vat.
Ko da ana tsiyaye ni kamar sadaka a kan hadaya da kuma hidimar bangaskiyarku, na yi farin ciki, kuma na yi farin ciki tare da ku duka.
18 Nanya nimon irume, anung wang dinayi abo, a iyitta nayi abo nin mi wang.
Kamar haka kuma sai ku yi farin ciki, ku yi farin ciki tare da ni.
19 Ama ndin cisu kibinayi kitin Cikilari Yesu a tuu Timitawus ku nayiri alele, meng wang nase likara asa nlaza nbelle mine.
Amma na yi niyya in aiko da Timoti wurin ku ba da dadewa ba, domin ni ma in sami karfafuwa idan na san al'amuran ku.
20 Bara na ndi nin mong tutung nafo ame ba, urika na adi nin nayi acine bara anunghe.
Gama bani da wani wanda halinmu yayi daidai da nasa, wanda yake juyayin ku da gaskiya.
21 Bara vat mine din pizuru imon nati minere, na imon Yesu Kristi ba.
Domin duka ribar kansu suke nema bata Yesu Almasihu ba.
22 Ama fe yiru imon ile na adi, nafo na gono asa asuu ucife katwa, nanenere ame di katwa nin mi nanya nlirun laiye.
Amma kun san darajar sa, kamar yadda da ke hidimar mahaifisa, haka ya bauta mani cikin bishara.
23 Ndin kpilizu ntuughe na nin molu kubi ba asa in yene ucin nimone kiti ninghe.
Shi nake sa zuciyar in aiko maku ba da dadewa ba idan naga yadda al'amura nake gudana.
24 Ama ndi ni kibinayi kirum nin Cikilari nworu meng liti ninghe wang ma dak na nin dadaunu ba.
Amma ina da gabagadi cikin Ubangiji cewa ni da kaina zan zo ba da dadewa ba.
25 Ama inyene ukifo gbas ntuu Epaparoditus ku ukpillu kiti mine. Ame gwana nighari nin don katwa ning udu likum ning, a gono kadura nin kucin nsuu ning.
Amma ina tunanin yakamata in sake aiko maku da Abafaroditus, shi dan'uwana ne, abokin aiki, da abokin yaki, manzon ku da kuma bawa domin bukatu na.
26 Bara awa lanza kuyamine kang, amini wa yita ni suu awadi amal zuru nan ghinu vat, anung na lanza na adi ucine ba.
Da shike yana marmarin ku duka, ya damu kwarai da shike kun ji yayi rashin lafiya.
27 Nanere, awa su kidowo kang nafo aba ku. Ama Kutelle na lanza nkunekune me, a na ame usamme ba, umunju mengku wang bara nwa se liburi lisirne kitene liburi lisirne.
Da gaske yayi rashin lafiya har ya kusan mutuwa. Amma Allah ya ji tausayin sa, ba shi kadai ba, amma har da ni, domin kada in yi bakin ciki kan bakin ciki.
28 Nene nkipina usuu nworu ntuughe, bara andi iyeneghe tutung imanin yitu nin nayiabo ima kalu njirjir nibinayi mine.
Domin haka na yi niyyar aiko shi, saboda idan kun sake ganinsa za ku yi farin ciki ni kuma in kubuta daga juyayi.
29 Seren Epaporoditus ku nin naburi abo nanyan Cikilari. Taan anit nafo ame ngongong.
Ku karbi Abafaroditus da dukan murna cikin Ubangiji. Ku ga darajar mutane irin sa.
30 Bara kitene katwan Kristiari awa lantin uku. Awa nari ulai me anan suyi katwa nin kulunu katwa kanga nafe wa yinnin usue ba nanyaa katwa ninghe.
Domin saboda aikin Almasihu ne ya kusan mutuwa. Ya sadakar da ransa domin ya bauta mani domin ya cika hidimar da ya kamata ku yi mani.

< Filibiya 2 >