< Yuhana 3 >

1 Nkon ku Farisawa wa duku lissame Nikodimus, awa di nin tigo nanya kudaru na Yahudawa.
Akwai wani Bafarisiye mai suna Nikodimus, wani ɗan majalisar Yahudawa.
2 Unit une wa dak kitin Yesu nin kitik a woroghe, “Rabbi, tiyiru fe unan dursuzu nanitari unuzu kiti Kutelle, bara na umong wasa asu ukama nilenge imone na udin suze se dei Kutelle di ninghe.”
Ya zo wurin Yesu da dad dare ya ce, “Rabbi, mun sani kai malami ne daga Allah. Gama ba wanda zai iya yin waɗannan abubuwan banmamaki da kake yi in Allah ba ya tare da shi.”
3 Yesu kawaghe aworo, “kidegenere andi na imara unit tutung ba, na awasa ayene kipin tigo Kutelle ba.”
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an sāke haihuwarsa.”
4 Nikodimu woroghe, “Ima kuru imaru unit inyizari na amal ti kukune? Na awasa apira liburi nna me imaraghe unba ba, awasa ayinnua?”
Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya za a haifi mutum sa’ad da ya tsufa? Tabbatacce ba zai sāke koma sau na biyu a cikin mahaifiyarsa don a haife shi kuma ba!”
5 Yesu kawa, aworo, “Kidegenere ndin bellu minu, andi na imara unit nanya nmyen nin Ruhu ba, na awasa apira nanya kipin tigo Kutelle ba.”
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
6 Imong ilenge na ina maru nanya kidowo, kidowari, a ilenge na ina maru nanya Ruhu, uruhuari.
Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
7 Na iwase uzikpu bara na nbellin minu, 'uso gbas ikuru imacu minu tutung.'
Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
8 Ufunu din ko udu kusari ko na unya udue. Asa ilanza uduwe, nani na iyiru kiti kanga na unuzu ku sa kiti kanga na udin cinu udue ba. Nanere wang unit ulenge na imaraghe nanyan Ruhu”
Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
9 Nikodimu kawa, aworo, “Inyizari imon ilele ma yitu nani?”
Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya wannan zai yiwu?”
10 Yesu kawaghe, aworo, “Fe unan dursuzu nanan Israila, vat nani, na uyinno ilenge imone ba?
Yesu ya ce, “Kai ma da kake malami na Isra’ila, ba ka fahimci waɗannan abubuwa ba?
11 Kidegenere, tidin belu ilenge imon nati yiru, ti din belu ilenge na tiyene, vat nani na anughe nsere uliru bite ba.
Gaskiya nake faɗa maka, muna magana a kan abin da muka sani, muka kuma shaida abin da muka gani ne, amma har yanzu kun ƙi ku karɓi shaidarmu.
12 Asa nbelin minu ubelen nimon nle uye a na anung yinna mun ba, ima yinnu inyizari nwa bellin ubelen nimon kitene kutelle?
Na yi muku magana a kan abubuwan duniya amma ba ku gaskata ba; to, yaya za ku gaskata in na yi magana a kan abubuwan sama?
13 Na umong nsa ghana kitene kani ba, se dei ulenge na ana tolu unzu kitene kani.
Ba wanda ya taɓa hawa zuwa sama sai wanda ya sauka daga sama, wato, Ɗan Mutum.
14 Nafo na Musa wa ghantin fiyii nanya ntene, nanere wang uso gbas i ghantin Usaun Nnit kitene.
Kamar dai yadda Musa ya ɗaga maciji a hamada, haka dole ne a ɗaga Ɗan Mutum,
15 Bara vat na lenge na iyinna ninghe nan se ulai unsali ligang. (aiōnios g166)
don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios g166)
16 Bara Kutelle nati usu inyii ulele, amini na ni gono kinin kirum cas, vat nlenge na ayinna ninghe, na ama nanu ba, ama se ulai un saligang. (aiōnios g166)
Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios g166)
17 Na Kutelle natu Gono me nanya nyie ada molu uyie ba, nani uyie nan se utucu unuzume.
Gama Allah bai aiki Ɗansa duniya don yă yi wa duniya hukunci ba, sai dai domin yă ceci duniya ta wurinsa.
18 Ulenge na ayinna ninghe na ima molughe ba. Ulenge na ayinna ninghe ba imal ciughe nca nkul bara na ayinna nin lissan Gono Kutelle ba.
Duk wanda ya gaskata da shi ba za a yi masa hukunci ba, amma duk wanda bai gaskata ba an riga an yi masa hukunci domin bai gaskata da sunan wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗan Allah ba.
19 ILenge imonere finu nsharawe, nworu nkanang na dak nanya inyii, anit ani nadi nin su nnsirti a na nkannanghe ba bara na adadumine an sirtiari.
Hukuncin shi ne, Haske ya zo cikin duniya, amma mutane suka so duhu a maimakon haske domin ayyukansu mugaye ne.
20 Bara vat nlenge na adin su adadu nsirti din su ivira tutung na ama dak kiti nkanangghe ba bara katwa me wa nuzu kanang.
Duk mai aikata mugunta yana ƙin haske, ba zai kuwa zo cikin haske ba don yana tsoro kada ayyukansa su tonu.
21 Vat nani, ulenge na adin su kidegen ma dak kitin kanang adadu me nan yita fang nyenju tutung inin damun ubun Kutelle unuzu nyinnu nin Kutelle.”
Amma duk mai rayuwa bisa ga gaskiya yakan zo cikin haske, domin a gani a sarari cewa ayyukan da ya yi an yi su ne ta wurin Allah.
22 Kimal nani, Yesu nin nono katwa me wa nya udu nmyin Yahudiya. Awa di dandaun kikane ligowe nanghinu acin shinto anit nmyen.
Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan Yahudiya, inda ya ɗan jima da su, ya kuma yi baftisma.
23 Yuhana tutung wadi nshitu nanite in Ayinon kupo in Salim bara nmyen wadiku gbardang. Anit wa dasu kitime a shinto nani nmyen,
To, Yohanna ma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salim, saboda akwai ruwa da yawa a can, mutane kuwa suka yi ta zuwa don a yi musu baftisma.
24 Na iwa di isa tursu Yuhana ku kilari licine ba.
(Wannan kuwa kafin a sa Yohanna a kurkuku.)
25 Mayardang fita kiyetik nnono katwa in Yuhana nin nkon ku Yahudawaaa in belen nwesu ulau.
Sai gardama ta tashi tsakanin waɗansu almajiran Yohanna da wani mutumin Yahuda a kan zancen al’adar tsarkakewa.
26 I do kiti in Yuhana i woroghe, “Unan dursuzu niyerte, ulenge na ani yita ninfi nleli ugau kurawan urdunghe, ame ulenge na uni su uliru kitene me, yene adin shintu anit nmyen, tutung vat din cinu kiti me.”
Sai suka zo wurin Yohanna suka ce masa, “Rabbi, wancan mutumin da yake tare da kai a ƙetaren Urdun, wannan da ka ba da shaida a kansa sosai nan, yana baftisma, kuma kowa yana zuwa wurinsa.”
27 Yuhana kawa nani, “Na unit wasa a sere imonmong ba, andi na inaghe unuzu kiti Kutelle ba.
Ga wannan zancen Yohanna ya amsa ya ce, “Mutum yakan karɓi kawai abin da aka ba shi ne daga sama.
28 Anung nin nati mine wasa ileoyi unanba, nlire na belle. 'Na meghari Kriste ba' nna woro, 'ina tuyi nbun mere.'
Ku kanku za ku shaida cewa na ce, ‘Ba ni ne Kiristi ba, sai dai an aiko ni ne in sha gabansa.’
29 Ulenge na adinin wani upese, unan kifu kudanari. Nengene udo tiyom, ulenge na ayisina alanza, asa asu liburi libo kang bara liwui kwanyane. Nengene liburi libo nin nkulo.
Ango ne mai amarya. Abokin da yake masa hidima yakan jira ya kuma saurara masa, yakan kuma cika da farin ciki sa’ad da ya ji muryar ango. Wannan farin cikin kuwa nawa ne, ya kuma cika a yanzu.
30 Uma so gbas ame kpizinku, meng cazin.
Dole ne yă yi ta ƙaruwa, ni kuma in yi ta raguwa.
31 Ulenge na ana dak unuzu kitene, di kinen vat. Ulenge na ana nuzu kutyin kunan kutyinari akuru adin belu nimon kutyin. Ulenge na ana nuzu kitene kani di kitenen koyan.
“Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa; wannan da ya zo daga ƙasa na ƙasa ne, yana kuma magana kamar wanda ya zo daga ƙasa ne. Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa.
32 Adin su uliru nimon ilenge na ana yene akuru alanza, nani na umon wasa asere uliru me ba.
Yana ba da shaidar abin da ya gani da kuma ya ji, duk da haka ba wanda ya yarda da shaidarsa.
33 Ulenge na asere uliru me ayinna Kutelle kidegenare.
Mutumin da ya yarda da ita ya tabbatar da cewa Allah mai gaskiya ne.
34 Ame ulenge na Kutelle na tughe din bellu uliru Kutelle. Bara na adin guccu uruhu me anin na unin ba.
Gama wannan da Allah ya aiko yakan faɗi kalmomin Allah ne, gama Allah yana ba da Ruhu babu iyaka.
35 Ucife dinin su Nsaune, amini nani imon vat nacara me.
Uban yana ƙaunar Ɗan ya kuma danƙa kome a hannuwansa.
36 Ulenge na ayinna nin Saune di nin lai nsali ligang, ame ulenge na ayinna nin Saune ba, ama yenu ulai ba, nani tinana nayi Kutelle sossin litime. (aiōnios g166)
Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios g166)

< Yuhana 3 >