< Katwa Nono Katwa 14 >

1 Nyan min Iconiun Paul nin Barnabas iwa piro kutii lira na Yawudawa, i belle tipipin Yise nin likara me. amini wa ti, a yahudawa nin na Greek i yinna nin tipipin Yesu.
A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
2 Vat nin nanin among a Yhudawe wa yinin ba, inin belle anan salin yinu Kutelle ba inari, ita nibinai nanan salinyinu Kutelle nan.
Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
3 Nin nan Paul nin Barnabas i ya don-don kite ne kan imini wa lira tipipin Kutelle sa fiu, amini wa ninani kaduran bolu Kutelle kana ti kamata ti se ba
Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
4 Vat nin nanin anite i wawuchu kidaw, among ima dofunu among nin belle indofunu nono kata Y bellin esu.
Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
5 Nin nanin anan salin yiri Kutelle, nin na yahudawa, i wa tinin risu na dida mine, inan taasu an Paul nin Barnabas,
Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
6 Dana ulire daa kutuf nan Bulus nin barnabas imini iwa chun ka gbire udu nmin [Kagbiri] Liconia, Listra nin Derba a usauran niti naana nidi pit ba.
Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
7 kikanare tutung an Paul nin barnabas iwa tinin bellu nani nin dursuzu ani tipipin Kutelle,
inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
8 Nan Listra umong unit wa diku salikara nabunu. Kubi kona uname wa marighe, na a sa tabina u sun chinba.
A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
9 Unit une wa lanza paul ku inliru, dana paul yeneghe, paul yinno, yinnume sau yenume matighe ashin.
Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
10 Amini wa belinghe nin liwui kan “fita nin nabunufe, “Ninnanin unite ghina nin nabunume atinan chinu.
sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
11 Dana anite yene ile imon na Bulus in su, ittunna ighantinna tiwui mine in belu nin tilem Nikoniyum “atelle abebene danari nafo anit.”
Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
12 Inin naa an paul nin Barnabas tisa, barnabase inaghe lisa “zeus”ame paul iyichilaghe nin lisa“harmas”bar ame wadi unanliru udiawe.
Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
13 Kutin prist zeus wadik kibulun kagbiri, ame nin anite, itina i nuzu kap udas nin nin Ninamine a tifulawa amomoagigimeichizina unakwizu usakirfais.
Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
14 Tutun Paul nin Barnabas lanza nanin inuzu nin kibinain kibibit nin jartina
Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
15 inin woro anite bar yanghari imasu ilaimone? bar nanin na iwa molu inamine ba, arikima anitari nafo anighe, tida mini nin liru uma, tidimun su ichin imon inazan ine idak kiti Kutelle un nan la, amare ulena anake kitene nin kutin ah kuli kubgardan
“Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
16 Nayirin burne, vat mine alenge na idi Ayahudawa ba wadin dortu namong atelle na iwa dinin suwe. Kutelle wa yinnin idortu nani bara na iwa yirughe ba.
A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
17 Ama awa durso nari nworu adin sunari katwa kacine. Amere asa ata uwuru ju, akuru ata imuse kunjo. Asa aamere tutung nafi imoli, ukuru akulo nibinayi mine nin nayi abo.
Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
18 Anite wa lanza imon ilenge na Paul nbelle, vat nin nani iwa yita nin su inakpiza ina ididya ine isu Paul nin Barnabas ku usujada. Ama udu nimalighe, anite kpiliza na isu ba.
Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
19 among a Ayahudawa, da unuzu Antiyok nin Ikoniyum, iwa dak ida risa anite gbardang nin nanan Listira inin nworu ilemon na Paul din bellu mimnu kinuwaridi. Anite na iyinna nin lire na Yahudawe tunna ilanza ayi nin Paul. Ita a Yahudawa tinnan filisu pau, inin kuru wunughe udu das kagbir, kikane iwa chiso aku
Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
20 Among na iwa yinni nin liru Kutelle Listira wa tinin iyisina ku popo Paul, kikane na awanonku kutinghe. Paul tunna azinto. Anin fita nya nin nanan yinnun nin liru Yesu inin pira ka gbire.
Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
21 Iwa so ita ayiri kikane ka, ile ubun bellu tipipin Yes, aniti gbardan wa yinin nin tipipinghe, nin kidu Paul nin Barnabas ita ubellen kwilu. inin kuru ida u Listira. inani wa kuru ikata udu Ikoniyum ini kuru ikata udu ka gbiri Antiyok nanya Pisidiya
Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
22 Vat kika na ipira iyatinin nizu linana likara nayi, na iwa lanza fiu ba, imini wa balin nanin yinu mine nin salin yenu itere kibinai mine nan ny, bar nanin nan nya tikanchi tona tinare matinari tipiru kitekane[kilari Kutelle]
suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
23 Paul nin Barnabas wa fere adidya nanya ligozin nanite. Nin tin bellen gniu nan nya nite Paul nin Barnabas inanin wa pitirin anite, i ta ayiri nan ghinu i nin ta ilira nin kifin unu[sauli ninmunli] nin nanin Paul nin Barnabas ininnakwa nanin kiti Kutelle udia urkana iwa yinin ninghe ama bunu nanin,
Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
24 Unuzu kidun, an Paul nin Barnabas, wa kata udu pisidiya inin da Upampiliya.
Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
25 Nanya kusa kone, inin lirina tipipin Kutelle nan ghe ka gbiri Perga innin kata udu Attalia.
kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
26 Kikanner, iwa nin pira ujirgi mmen intina i kwiila udu Antakiya, nanghe kagbiri in Siriya. Kagbiri kanere iwa fere Paul nin Barnabas do nnan niti idi su uwaze ku, tutung niti nanga anan yinnu nin Yesu wasu nlira Kutelle bun Paul nin Barnabas nanya katwawe na ina malu nene.
Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
27 Kubikono iwadak nanya Antiyok inin yichila anan yinnu sa uyenu kitikirum, inin belle elemon na Kutelle nasu nin punu kibulun udu iktinanan salin yinu Kutelle ini selibou lirika longo na lima du nin ghinu kitene nin yinnu yesu
Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
28 Nin nanin Paul nin Barnabas wa dodon nin nono kata Kutelle
Suka kuma jima a can tare da almajirai.

< Katwa Nono Katwa 14 >