< 1 Bitrus 2 >

1 Bara nani ceon adadu ananzan likot vat, urusuzu liti, nshina nin liru uhem.
Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
2 Nafo nono nipesse, idi ntok mmazin milau min ruhu, inan kunjo nan nya utucu minin,
Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
3 andi ina ciro ise cikilarie di nin kibinai kisheu.
yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
4 Dan kiti nlenge na amere litala nlai longo na anite na nari, ama Kutelle na fere linin nloli di ghe gongong.
Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
5 Anung wang masin nafo alala nlaiyari alenge na ina kye iso nilari nruhu, inan so a pristoci alau na ima nakpizu uhadaya nruhu ulenge na Kutelle ma seru unuzun Yesu Kristi.
ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
6 Uliru ntuce nworo nenge, “lanzang nna nonko nsihiyona litala liguda kutyi, lin cizunu, licine a licaut. Ulenge na a yinna ninghe na aina ti ncing ba”.
Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
7 Ngongonghe min fere na uyinna ama, “litala na anan kye kutiye wa nari, linnare nso litala liguea kutiye”
A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
8 a litala ntirzu a kuparang ntirizu” I tirzo, inari uyinnu nin lirue, ulenge na imung wang iwa fere nani mun.
kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
9 Anung imus nferuwari, a pirist tigo, nmyin milau, annit Kutelle an litime, inan belle katwa kazikiki nlenge na ana yicila minu unuzu nan nya nsirt ucindu nan nya nkanang mi zikiki.
Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
10 Na iwa mandi anit ba, ana nene idi anit Kutelle. Na iwa seru nkunekune ba, ama nene ina seru nkunekune.
Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
11 Yenen, nna yicila minu nafo amara nin na nan galu inan wantina atimine ntok nalapi, alenge na adin su likum nin tilai mine.
Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
12 Yitan nin nadu a cine nan a cine nan nya na nan salin dortu Kutelle, bara, asa isu uliru na timine nworu ina su imon inanzang, ima su seng izazin Kutelle lirin nsa me.
Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
13 Nonkon ati nin tigo nanit vat bara likilari, sa ugo na amere udya vat,
Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
14 sa anan tigo na ina tu nani ida ti anan nalapi ineo inin zazin alenge na idin sa katwa kacine.
ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
15 Bara nanere usu Kutelle, nan nya nsu nimon icine itursu uliru tinu nanit alalang.
Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
16 Nafo ale na idi licin ba, na iwa su katwa nin salin yitulicin mine imon tursuzu katwa ka nanzang, ana son nafo acin Kutelle.
Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
17 Ghantiuan anit vat. Tan usu linuwana, tan fiue Kutelle ghantinan Ugo.
Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
18 Acin, nan nibinai mine kiti nan cinilari mine nan nyan nonku nati, na kiti nan cinilari acine cas ba, umunu a nanazanghe wang.
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
19 Bara imon ngongonghari asa umong ntere kibinai nan nyan konu a ayita nniu asa i waso uliru na dert ba bara uni litime kiti Kutelle.
Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
20 Mmari mi mashinari diku uwa ti kulapi unin ti anyi akona kubi nhoro? Ama asa uta imon icine umin nneo kubin horo, ilele imon ngongonghari kiti Kutelle.
Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
21 Kiti nilelere iwa yicila minu, Kristi wang na sono unin bara anughe, amini na sun udursuzu nworu among dofin libo me
Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
22 Na an ti kulapi ba; a na ina se kinu nnu me ba.
“Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
23 Na iwa zogoghe, na awa tunu izoge ba, na awa neo, na nan tunu uniwe ba, ama ana ni litime kiti nlenge na adin su ushara dert.
Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
24 Ame litime na yaun alapi bite kidowo me udu kitene kuca, bara arik wa kuru ti se ndinong kulapi, arik nan se tiso anan sali na lapi. Bara anit kidowo me ina se ushinu tikonu mine.
Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
25 Vat mine na galu nafo akam nwulu, ame nene ina kpilin kiti nnan libyawe nin nan yenju tilai mine.
Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.

< 1 Bitrus 2 >